Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Tor Tiv Ya Yabawa Farfesa Adamu Gwarzo Bisa Kafa Jami’ar MAAUN

  Sarkin kasar Tiv wanda aka fi sani Tor Tiv of Tiv, Farfesa James Ortese Ayatse, ya jinjinawa shugaba kuma mu’assasin Jami’ar Maryam ...

 


Sarkin kasar Tiv wanda aka fi sani Tor Tiv of Tiv, Farfesa James Ortese Ayatse, ya jinjinawa shugaba kuma mu’assasin Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN), ta Nijeriya dake Kano bisa kafa jami’ar tare da samar mata da kayan aiki na zamani.

Sarkin gargajiyar ya jinjinawa Farfesa Gwarzo ne a yayin da ya kai ziyara a jami’ar dake Hotoro a cikin kwaryar Kano da yammacin ranar Juma’a.

Sarkin kuma shugaban al’umma, an jagorance shi inda aka zagaya da shi tsangayoyin jami’ar daban-daban tare da sassan jami’ar, dakunan karatu, wuraren bincike, ajujuwan karatu, ginin gudanarwa na jami’ar, ofisoshi dake cikin jami’ar, inda ya yabawa wanda ya samar da jami’ar bisa wannan himma da kokari.

 “na yi matukar jindadi da wannan tsarin. Na yi farin ciki bisa yadda na ga gine-ginen da aka yi. Suna da aiki da nagarta”, inji Sarkin.

Har wala yau Basaraken ya shawarci hukumar gudanarwa na jami’ar da su kafa cibiyar sadarwa da fasahar zamani domin taimakawa jami’ar wajen samun karbuwa, ingancin dalibai tare da kuma hanyar bunkasa koyarwa da bincike.  

Sannan ya nemi wanda ya kafa jami’ar ta MAAUN da ya ci gaba da maida hankali bisa kyawawan tsare-tsaren da ya shimfida musamman wajen bunkasa tsarin tare da ci gabantar da bangaren ilmantarwa da kuma kayayyakin da aka sanya.

 “a matsayina na Basarake kuma Farfesa da yake da masaniya wajen gudanar da jami’a, na yi matukar jindadi da abin da na gani”, ya tabbatar.

Ya kara da cewa; “a don haka, akwai bukatar samar da kudaden da za a ci gaba da kyawawan ayyukan da aka faro domin gudun tsayawar aikin”, ya lurantar.

Ya yi alkawarin bayar da duk wata dama a kowanne lokaci domin yin lurantarwa da kuma bayar da shawara a muhimman abubuwan da jami’ar ke bukatar mayar da hankali a kai tun farko don ba ta damar cimma nasarar da ake bukata.

Honorabul Prince Moses Ternenge yana daga cikin wadanda suka raka Basaraken Farfesa Iorzua Ortese James Ayatse a ziyarar da ya kai jihar Kano.

 

Basaraken ya ce ya zo ne Kano ne domin halartar taron nadin sarauta ta Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, inda ya yanke shawarar duba abin da ke gudana a wannan jami’ar ta duniya.

 

No comments