Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Al’ummar Jihar Katsina Sun Yi Kira Da A Dawo Musu Da Sadarwa

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari -Hakan ya lalata kasuwancinmu, inji wani dan kasuwa Daga Ammar M. Rajab Al’ummar jihar Katsina...

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari


-Hakan ya lalata kasuwancinmu, inji wani dan kasuwa

Daga Ammar M. Rajab

Al’ummar jihar Katsina mazauna kananan hukumomin da yanke sadarwa ya shafe su sun yi kira ga gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari da Hukumar sadarwa ta Nijeriya, NCC da sauran hukumomin tsaro da su dubi Allah su dawo musu da sadarwa a jihar domin a cewarsu hakan ya kuntata rayuwarsu tare da dakile ci gaban harkokinsu.

Al’ummar sun koka ne a yayin zantawarsa da MADOGARA a yau Litinin, inda suka shaidawa wakilinmu cewa duk da datse sadarwar da aka yi hakan bai hana ‘yan bindigar ci gaba da kai hare-hare da kuma garkuwa da jama’a ba.

Jihohin Sakkwato da Kaduna tuni suka dawo da sadarwar bayan da farko an datse, a yayin da jihar Zamfara tun a cikin watan Oktoba aka dawo da na babban jihar wato Gusau, inda kuma gwamnan ya bada tabbacin cewa a gobe Talata za a dawo da na sauran kafatanin kananan hukumomin jihar.  

A cikin watan Satumban 2021 ne, kimanin wata 3 ke nan, yau ana da adadin kwanaki 89 da katse sadarwa a kananan hukumomi sha uku (13) na jihar. Hakan ya biyo bayan zafafa hare-hare da ‘yan bindiga suka rika kai wa a jihar ta Katsina.

Gwamnan jihar, Aminu Bello Masari ne ya bai wa kamfanonin sadarwa a Nijeriya umurnin datse sadarwar wanda a cewar sanarwar gwamnati, hakan zai bai wa hukumomin tsaro damar yaki da ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da kuma masu garkuwa da mutane da suka addabi jihar.

Kananan hukumomin da aka datse sadarwar sune; Sabuwa, Faskari, Dandume, Batsari, Danmusa, Kankara, Jibia, Safana, Dutsin-Ma, Funtua, Bakori, Malumfashi da Kurfi.

Sai dai wani dan kasuwa mazaunin garin Dandume dake karamar hukumar Dandume, da ya nemi a sakaya sunansa ya shaidawa wakilinmu cewa yanke sadarwar da aka yi ya tsayar da kasuwancinsu na sayar da hatsi, wanda ya ce ba shi kadai ba, dukkanin abokan kasuwancinsu sun jiggata a tsawon wannan lokacin, inda ya yi kira da a dawo musu da sadarwar; “wannan yanke sadarwar ba ma ni kadai ya shafa ba, ya shafi dukkanin wani alakar kasuwanci dake babbar kasuwar Dandume ta hatsi musamman da sauran kasuwanni. Kamar mu da muke kasuwar ‘yan hatsi, muna sayen wa mutane kaya ne daga Kudu, su turo kudi a saya musu kaya a tura musu, yanke sadarwar nan ya kai ga cewa kasuwa ta lalace. Ta yadda lokacin da ake tunain a bi kadari, talaka ya samu wani abu, sai ya zama na ba masu saye gaba daya”, ya tabbatar.

Ya ci gaba da cewa; “wani lokacin yana zama ba halin waya, sai dai ka tashi ka tafi har Zariya sannan ka yi waya. Sannan idan ka je Zariya mutanen sun sanya maka kudinsu, ka taho a hanya kana fargaba saboda za ka iya kai wa yamma, kuma ga yanayin tsaro na hanya din. Maganar gaskiya yankewa din ya dagula duk lamarin kasuwanci dake garin Dandume da ma yankinmu gaba daya!”, ya tabbatar.

Shi kuma wani mazaunin Abuja mai suna Yahaya Muhammad Abdullahi a zantawarsa da wakilinmu ya koka mana cewa; “yanke sadarwar nan an yi min katangar karfe da sauraren masoyiyata wanda sauran watanni kadan suka rage mu yi aure. A halin yanzu ba na jinta, ban san halin da take ciki ba, abubuwan shirye-shirye na biki sun tsaya saboda ba tattaunawa a tsakaninmu”, ya furta cikin yanayi na damuwa.  

Shin kwalliya ta biya kudin sabulu?

Wani dan kasuwa mazaunin Dandume, da ya nemi a sakaya sunansa ya ce yanke sadarwar ba haifar da da mai ido ba, a cewarsa; “babu wani kwalliya da ta biya kudin sabulu, bai biya ba. Saboda duk kauyakun da ake tunanin ‘yan bindigar na kai hare-haren, babu inda ba su shiga ba, sun yi ta’addancinsu ba tare da duniya ta ji me suka aikata ba saboda babu sadarwa. Ko kwanan nan sun kai wani hari ya ma shafi wadansu abokanmu, an yi abin sai bayan kwana biyu, aka ji ma labarin abin da ya faru. Ina amfanin yanke sadarwar? Bai biya ba gaskiya, kawai ana azabtuwa ne!”, ya jaddada.

Sai Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Mustafa Inuwa, a taron manema labarai da ya kira a kwanakin baya a lokacin da rahoto ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun fara amfani da oba-oba wajen sadarwa a tsakaninsu sakamakon yanke sadarwar,  ya ce tabbas suna da labarin hakan, kuma tuni jami’an tsaro suka dukufa tare da masana domin ganin cewa sun hana ’yan ta’addan yin amfani da wannan na’ura wadda ake zargin wasu bata-gari ne ke samar musu ita ko kuma ta hanyar saye ta intanet a cewarsa.

Sai dai a cewarsa yanke sadarwar tuni kwalliya ta fara biyan kudin sabulu duk kuwa da halin kuncin da jama’a suke fuskanta wanda ya ce sai an yi hakuri kafin ganin an samu nasara a kai.

A cewarsa; “Kadan daga cikin irin nasarorin da wannan dokar ta samar sun hada da hana samun bayanai daga masu ba su labari a kan inda za su kawo hari ko shigar jami’an tsaro domin kai musu farmaki.

“Yin garkuwa da mutane ya yi sauki fiye da baya; dokar ta rage yawan kwacen babura da kuma shigar musu da man fetur da suke amfani da shi suna zubawa ababen hawansu.”

Sakataren gwamnatin ya kara da cewa, idan aka lura daga lokacin kafa dokar zuwa yau, misali a tsakanin watan Yuli da Agusta na 2021 an samu rahotannin yin garkuwa da mutane har 173 wanda ya shafi mutane 475.

Amma a tsakanin watan Satumba da Oktobar 2021 an samu rahoton garkuwa da mutanen sau 61 wanda ya shafi mutane 102 kamar yadda Aminiya ta labarto.

Me masana ke cewa kan datse sadarwar?

Su kuma masana a Nijeriya na bayyana damuwa kan matakin da gwamnatin Nijeriya ta ɗauka na toshe hanyoyin sadarwar.  

Malam Kabiru Adamu, wani masanin harkokin tsaro na ganin cewa an sha ɗaukar irin waɗannan matakan amma ba tare kawo ƙarshen matsalar tsaron ba. Kuma toshe layukan sadarwar zai yi matukar tasiri ga jefa mutanen yankin cikin mawuyacin hali.

Haka kuma masanin ya ce ƴan bindigar za su iya amfani da hanyoyin sadarwa na tauraron ɗan adam da kuma intanet. Don haka suna da zaɓi na hanyoyin da za su yi amfani da su domin sadarwa, a cewarsa.

Sannan matakan a cewar masanin za su shafi tattalin arziki da jefa jama'a cikin wahala.


-Rahoton MADOGARA

No comments