Shugaban Algeria AbdelMajid Tebbourne ya haramta fitar da kayayyakin abinci zuwa kasashen ketare a daidai lokacin da ake ci gaba da fargab...
Shugaban
Algeria AbdelMajid Tebbourne ya haramta fitar da kayayyakin abinci zuwa
kasashen ketare a daidai lokacin da ake ci gaba da fargabar tashin farashin
kayayyakin abinci saboda rikicin Rasha da Ukraine, yayin da masana ke cewa,
matsalar ka iya haifar da yunwa a kasashen Larabawa.
Kayayyakin
abincin da Algeria ta haramta fitar da su sun hada da Sikari da Man-gyada da
Taliya da Garin Masara na Semolina da kuma sauran nau’ukan abincin da ake samar
da su daga alkama.
Shugaban
na Algeria ya dauki matakin ne bayan ya saurari jawabin da Ma’aikatun Noma da
Kwadago na kasar suka gabatar masa game
da abincin da aka fi ta’ammulli da su a kasar.
A
bangare guda, rahotanni na cewa, iyalai da dama a daukacin sassan yankin Arewacin Afrika na ci gaba da
rige-rigen sayo nau’ukan abinci irinsu filawa da garin masara suna adana su,
saboda fargabar tashin farashin abinci a dalilin yakin Rasha da Ukraine.
Wannan
na zuwa ne a daidai lokacin da ya rage ‘yan makwanni a fara gudanar da azumin
watan Ramnadan, lokacin da iyalai suka fi wadata kansu da abinci.
Tunisia
da Morocco da Libya da sauran kasashen Larabawa, na shigo da alkama ne daga
Rasha da Ukraine da ke gwabza yaki a yanzu haka, abin da ya sa ake ganin cewa,
babu shakka wannan tashin hankalin zai jefa yankin na Arewacin Afrika cikin
wani mummunan yanayi na karancin abinci.
Wasu
ma na fargabar cewa, yakin na Rasha da Ukraine zai haddasa yunwa da kuma
tarzoma a kasashen Larabawa, kamar dai yadda aka taba gani shekaru 10 da suka
wuce.
No comments