Daga Awwal Umar Kontagora Kungiyar Matasan Jam’iyyar APC da kuma tuntuba ta yi Allah-wadai da jam’iyyar PDP kan zargin da ake yi wa karamin ...
Daga Awwal Umar Kontagora
Kungiyar Matasan Jam’iyyar APC da kuma tuntuba ta yi Allah-wadai da jam’iyyar PDP kan zargin da ake yi wa karamin ministan tsaro, Honarabul Bello Mohammed Matawalle da muzgunawa ‘yan adawa a yankin Arewa maso Yamma.
Shugaban kungiyar, Alhaji Ashiru Tukur, ya bayyana zargin a matsayin farfagandar siyasa mara tushe kuma arha da nufin bata sunan gwamnatin APC. Ya bukaci dattawan jam’iyyar PDP da su maida hankali wajen magance rikicin cikin gida a maimakon yin zarge-zarge marasa tushe.
Alhaji Tukur ya bayyana cewa jam’iyyar PDP tana da tarihin gazawa wajen kawo rashin zaman lafiya a siyasan ce. Ya yabawa Minista Matawalle a matsayin mai bayar da tallafi ga wadanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su a jihar Zamfara, duk da cewa yana fuskantar tsangwama daga Jam'iyyar PDP a jihar da matakin kasa.
No comments