Daga Zailani Mustapha Mabiya Harkar musulunci a Nijeriya wadanda aka fi sani da 'yan shi'a sun bayyana cewa; jami'an tsaron ...
Mabiya Harkar musulunci a Nijeriya wadanda aka fi sani da 'yan shi'a sun bayyana cewa; jami'an tsaron 'yan sandan Nijeriya sun afkawa masu tattakin arba'in na Imam Husaini a birnin Tarayya Abuja.
Wannan sanarwar na dauke ne a wata takardar manema labarai da Sheikh Sidi Munir Mainasara Sokoto ha sanyawa hannu a madadin Harkar Musulunci a Nijeriya a karkashin Shaikh Ibraheem Zakzaky a ranar Lahadi 25 ga watan Agustan 2024.
Takardar ta soma da cewa; "Muna so mu sanar da al’umma
cewa ‘yan sanda sun kai farmaki kan tattakin Arba’een da yake gudana a Wuse a
birnin Tarayya Abuja tare da kashe mutane da dama. A yayin da ake kokarin
tarwatsa masu tattakin na Arbaeen, ‘yan sandan sun kashe tare da raunata masu tattakin
da dama", in ji sanarwar.
Sanarwar ta ci gaba da cewa; "A halin yanzu, jami'an
tsaro sun shagaltu da kama masu tattakin.
"Likitoci na kula da
wadanda suka samu munanan raunuka, kuma za a gabatar da cikakkun bayanai na
wadanda aka kashe, da wadanda suka jikkata, da kuma wadanda aka kama ga manema
labarai nan gaba kadan.
"Kafin a fara tattakin,
mun binciki dukkan mahalarta taron domin tabbatar da cewa babu kutse, kuma taron
zai kammala kamar yadda aka tsara.
"Tattakin Arbeen din da
aka gudanar a jiya a yankin Masaka da Zuba ya kare lafiya kuma cikin nasara", sanarwar ta karkare.
No comments