Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

APC Ta Lashe Duka Ƙananan Hukumomi 13 A Zaɓen Jihar Nasarawa

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulkin jihar Nasarawa ta lashe kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 13 na jihar da aka yi. Shu...



Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulkin jihar Nasarawa ta lashe kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 13 na jihar da aka yi.

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Jihar Nasarawa (NASIEC), Barr. Ayuba Usman, shi ne ya bayyana hakan a hedikwatar hukumar da ke Lafiya,babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa baya ga kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 13, ƴantakarar jam’iyyar APC sun lashe kujerun kansila 140, yayin da jam’iyyar SDP ta lashe biyar, sai kuma Zenith Labour Party (ZLP) ta lashe biyu.

Kujerun kansilolin ZLP biyu suna cikin ƙaramar hukumar Doma, na SDP huɗu a Nasarawa-Eggon, da kuma ɗaya a ƙaramar hukumar Keffi.

Ya ce jam’iyyun siyasa 14 ne suka fafata a zaben, yana mai cewa amfani da fasaha ya ƙara sanya zaɓen ya kasance mai inganci.

No comments