Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Shaikh Zakzaky Ya Samu Karramawa Bisa Gagarumin Gudummawar Da Yake Bai Wa Bangaren Ilimi

Daga Zailani Mustapha  Bisa ga irin gagarumar gudummawar da yake bayarwa wajen inganta rayuwar matasa da mata, Shikh Ibraheem Zakzaky ya sam...


Daga Zailani Mustapha 

Bisa ga irin gagarumar gudummawar da yake bayarwa wajen inganta rayuwar matasa da mata, Shikh Ibraheem Zakzaky ya samu lambar yabo mai daraja ta "Best Philanthropic and Humanitarian Service for Development for Women's Education in the Nation 2024" ta ƙungiyar tallafawa shirin matasa da mata ta ƙasa (NYWSIF).

Sanarwar ta fito ne a wata takarda mai ɗauke da sa hannun Ambasada Abdullah Ibrahim Saraki, shugaban NYWSIF na ƙasa.

Ƙungiyar ta yabawa Shaikh Zakzaky bisa namijin ƙoƙarin da yake yi wajen bunƙasa ilimi da kuma da inganta rayuwar matasa da mata a faɗin Nijeriya.

NYWSIF, ta kuma yaba da tsarin jagoranci, da shiriya, da kuma gudummawar Shehin Malamin wajen yadda yake inganta rayuwar al'umma.

A yau Laraba 29 ga watan Junairun 2025 ne Æ™ungiyar ta ziyarci Shaikh Zakzaky a gidansa dake Abuja domin gabatar masa da lambar yabo a hukumance. Sun bayyana Æ™oÆ™arin nasa a matsayin wanda ba zai iya misaltuwa ba, sun kuma bayyana yadda sadaukarwarsa ta Æ™ara zaburantar da al’umma wajen saka hannun jari a fannin ilimi da ci gaban matasa.

Ƙungiyar ta rubuta wata jimla a cikin wasiƙar, inda ta ce "Albarka Tana Wurin Manya", wanda ke nuni da matuƙar albarkar da suke nema a kan aikin su.

Da yake jawabi a madadin ƙungiyar, Ambasada Saraki ya miƙa godiyar sa ga Sheikh Zakzaky "bisa gudummawar da yake bayarwa wajen ciyar da ilimin mata gaba."

Bikin karramawar ya nuna irin tasirin da Shehin Malamin ya yi ga rayuwar ‘yan Nijeriya da daman gaske.

A nasa jawabin, Shaikh Zakzaky ya buƙaci ƙungiyar da ta ci gaba da kasancewa a kan gwadaben ayyukan raya al'umma musamman matasa da mata a faɗin ƙasar nan, tare da tafiya bisa manufofinsu da suka zayyana na samar da makoma mai kyau ta hanyar ilimi da tsare-tsare masu kyau na ci gaba.

Kazalika ya shawarce su da su ji tsoron Allah a dukkanin al’amuransu.

No comments