Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce har yanzu shi ɗan jam'iyyar PDP ne duk da cewa ya soma tattaunawa da jam...
Tsohon gwamnan jihar
Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce har yanzu shi ɗan jam'iyyar PDP ne duk
da cewa ya soma tattaunawa da jam'iyyar NNPP domin sauya sheka zuwa can.
A hirarsa da BBC,
jagoran kungiyar siyasa ta Kwankwasiyya ya ce a makwannin da suka gabata ne suka
kaddamar da wata sabuwar kungiya mai suna 'The National Movement', bayan nan ne
aka samar da jam'iyyar NNPP wato New Nigeria People Party ma'ana dai sabuwar Nijeriya.
Kwankwaso ya ce, wannan
sabuwar jam'iyya ce ta mutanen da suka amince cewa akwai bukatar tsarin da aka
taho da shi daga shekarar 1999 a sauya shi a kawo abin da jama'a za su amfana.
Ya ce akwai bukatar
nazari kan abin da kasa za ta sauya sannan ta samu sabon alkibla, sai dai yana
mai jaddada cewa har yanzu ya na nan a cikin jam'iyyar PDP bai fita daga
cikinta ba.
''A yanzu maganar da
ake yi ina cikin jam'iyyar PDP, tun wancan lokacin mun fara abin hawa-hawa.
Abu na farko da muka
fara yi shi ne ja baya daga tsarinta, tunanin wasu masu hankali za su zo a
zauna a fada musu abin da ya dame mu amma jam'iyya ba ta yi ba, muka shiga
kungiya nan ma ba a yi komai ba, to gamu a matakin jam'iyya.
Har yanzu da na ke
magana da kai muna tsakanin kungiya da jam'iyya sannan ban fita daga cikin
jam'iyyar PDP ba, kuma wannan kungiya ta hade ne da jam'iyyar NNPP.
Duk ranar da zan bar
PDP ku ne na farko a za ku sani saboda abubuwan ne a tsare su ke mu na komai
cikin tsanaki.''
Kwamkwaso ya ce ba wai
ya raba kafa ba ne tsakanin jam'iyyar NNPP da PDP kuma idan manyan jam'iyyar
PDP suka bukaci a sasanta tsakaninsu ya ce yanayin zai danganta da abin da suka
fada da kuma yadda su sauran abokan tafiya suka kalli lamarin.
''Maganar ba ta Rabi'u
Kwankwaso ko ta Kwankwasiyya ba ce, magana ce ta 'The National Movement' kuma
muna da yawa a ciki, sannan yawancin wadanda ke cikin ta manyan mutane ne dan
haka ba zan yanke hukunci ni kaɗai ba.''
Da aka tambaye tsohon
gwamnan kan rahotanni da ke cewa an rushe shugabancin jam'iyyar NNPP tun ma
kafin su shige ta da kuma kakkabe duk wanda ba ɗan Kwankwasiyya ba da yin sabon
zubi da 'yan Kwankwasiyya sai ya kada baki ya ce:
''A'a ai jam'iyyar
daman ba ta mu ba ce, amma ana son mu zo a tafi tare dan haka su na son mu kawo
namu su ma su kawo nasu.
Sannan lokacin
shugabancinsu ya wuce don haka kowa ya sauka, ciki har da shugaban da ya yi
mata rijista sama da shekara 20 da ta wuce.
Dan haka tsari ne ake
hadawa da namu da nasu saboda mafi yawan jihohi ba su da kowa,'' in ji
Kwankwaso.
Kafuwar TNM
A watan Fabrairu da ya
wuce ne Sanata Kwankwaso ya jagoranci wani gagarumin taro na wasu manyan 'yan
siyasar kasar karkashin wata kungiya mai suna 'The National Movement', TNM.
Fitattun mutane da 'ƴan
siyasa da suka halarci taron sun haɗa da Alhaji Tanko Yakasai da Capt Idris
Wada, tsohon gwamnan Kogi da tsohon sakataren watsa labarai na jam'iyyar PDP
Rufai Alkali.
Akwai kuma irinsu Aminu
Ibrahim Ringim, tsohon ɗan takarar gwamna a jihar Jigawa da kuma Inijiniya Buba
Galadima.
An gudanar da taron ne
a babban dakin taro na International Conference Centre da ke Abuja, babban
birnin tarayyar Nijeriya.
A jawabin Kwankwaso, ya
ce wasu 'ƴan kasar ne da suka damu da abin da ke faruwa a ƙasar suka haɗa kai
don ceto ta daga mawuyacin halin da ta shiga.
Ya ce yunƙuri ne na
'ƴan Nijeriya masu kishi da suke zaune a gida da ƙasashen waje.
Sharhi
Sanata Kwankwaso, wanda
fitaccen ɗan siyasa ne da ke jam'iyyar hamayya ta PDP, ya dade yana kokawa kan
matsalolin da ke addabar Nijeriya da kuma abin da ya kira ''rashin mayar da
hankali'' daga ɓangaren gwamnatin jam'iyyar APC na shawo kansu.
Kazalika, ya sha yin
korafi kan wasu matsaloli da ke faruwa a cikin jam'iyyarsa ta PDP, wadanda ya
ce shugabanninta sun kasa magancewa domin a tsayar da dan takarar da "zai
iya kai jam'iyyar ga nasara" a zaɓen da ke tafe.
Hakan ne ya sa wasu
suke ganin tsohon gwamnan na jihar Kano ya ke jagorantar yunkurin "kawo
gyara" a harkokin siyasar Nijeriya ta yadda 'yan kasar za su samu ci gaba.
Abin jira a gani a halin da ake ciki dai, shi ne lokacin da zai sanar da ficewa daga jam'iyyar PDP mai hamayya a Nijeriyar.
-Rahoton BBC Hausa
No comments