Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Gwamna Bago Ya Samar Wa Neja Tagomashi Da Martabar Da Ba Gwamnatin Da Ta Samar Da Shi Tun Kafuwar Jihar - Bobi

  Daga Awwal Umar Kontagora Shugaban jam'iyyar APC a jihad Neja, Hon. Aminu Musa Bobi ya bayyana cewar gwamnatin manomi Rt. Hon. Uma...

 


Daga Awwal Umar Kontagora

Shugaban jam'iyyar APC a jihad Neja, Hon. Aminu Musa Bobi ya bayyana cewar gwamnatin manomi Rt. Hon. Umar Mohammed Bago ta samarwa jihar Neja martaba da tagomashin da ba wata gwamnatin da ta samar da irinsa tun bayan kafuwar jihar. Shugaban ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da gwamnatin ke cika shekara daya kan madafun ikon jihar.

Bobi, ya cigaba da cewar bayan zuwan Bago kan karagar mulkin jihar wanda uba ne kuma cikakken dan jam'iyyar APC ya kafa dambar gina hanyoyi guda dari biyar da ashirin da shi a fadin jihar, wanda manyan kananan hukumomin jihar kamar Suleja, Kontagora da Bida dukkansu zasu samu kaso na aikin hanya kimanin kilo mita talatin da biyar zuwa arba'in da biyar yayin da sauran kananan hukumomi zasu ci ribar kilomita biyar zuwa sama, wanda a halin yanzu ba karamar hukumar da ba a fara aikin ba.

Idan ka dawo shalkwatan jiha, wato Minna za a gina hanyoyi kilomita dari da doriya, wanda tun daga karamar hukumar Paikoro zuwa cikin garin ko wanda bai san fadar gwamnatin jiha zai shaidi cewar an samu gwamnati mai kishin cigaban jihar nan.

Wannan ne ya janyowa jihar Neja, kambin yabo da girmamawa idan ka kwatanta da jahohin yankin arewa ta tsakiya, wanda sauran gwamnoni da shugabannin jam'iyya sun yaba da irin yunkurin Mohammed Bago na martaba jam'iyyar nan a wannan yankin.

Bayan zuwan Umar Bago, ya bada political appointment sama da dubu takwas ga yayan jam'iyya, wanda dan abinda ake amsa na hakkin jam'iyya daga albashin masu mukaman siyasa daga tarayya har zuwa kananan hukumomi, shi muke tattarawa muka biya bashin kudin haya na kusan shekaru hudu da ake bin mu, bayan nan mun baiwa yayan jam'iyya sama da dubu bakwai appointment wanda mai karamin albashi na karban naira dubu arba'in.

Bisa kwarin guiwar da wannan gwamnatin, yasa muka himmantu wajen kafa wani abu na tarihi da zai karawa jam'iyya samun gindin zama da karbuwa na samar da sakatariyar jam'iyya mai zaman kan ta, wanda a tarihin Afrika ba za a samu irinsa, wanda muke sa ran kashe sama da naira biliyan biyu a ginin sakatariyar jiha kawai.

Saboda haka, kudurin mu shi ne duba da kyakkyawar manufa da burin da gwamna Bago yake da shi a jihar nan, da sauyin da ya kawowa siyasar jihar nan, dukkanin wadanda suka samu appointment daga matakin tarayya zuwa kananan hukumomi har wanda jam'iyya ta bayar mutane ne da idan lokacin zabe yazo 2027 zasu iya kawo kuri'un wasu wanda abinda zamu nema ciko ne dan gwamna Bago ya cigaba da jan ragamar jihar nan.

Abinda muke kuduri idan Allah ya ba mu aron rayuwa, kamar yadda gwamna ya aza tubalin ginin jihar nan, a bangaren hanyoyi, kiwon lafiya, da dawo da martabar noma da kiwo, shi ne goya masa baya a 2027 dan cigaba da wadannan ayyukan na alkhairi a jihar Neja.

Da yardar Allah, muna tsare tsaren da jam'iyya da kan ta za ta sayawa gwamna fom dan samun zagon na biyu ba tare da hamayya ba, wanda duk wani zababbe da ya taka rawar gani wajen kawo cigaba a jihar nan da jam'iyyar APC za mu tabbatar jam'iyya ce ta zama gata gare shi dan cigaba da ayyukan alheri na ayyukan raya kasa a jihar nan.

Hon. Aminu Bobi, ya jawo hankalin yayan jam'iyyar APC da su kara azama wajen gina jiha da jam'iyya, su watsar da batutuwan yan adawa domin adawarsu ba zai hana gwamnati cigaba da ayyukan da ta sanya a gaba ba, fatar wannan gwamnatin bisa jagoranci uba kuma cikakken dan jam'iyya shi ne samar da sabuwar jihar Neja.

Matasa sun rungumi hanyoyin dogaro da kai, gwamnati za ta samu kwarin guiwa wajen kawo ayyukan alheri da samar da abubuwan more rayuwa da aka yi mana tazara ne muddin matasa suka zama masu kishin kan su da kasa ne, wanda akwai zaratan yan siyasa masu kawo shawarwari nagartattu da gwamnatin jiha ke anfana da su wajen gina jiha.

No comments