Daga Zailani Mustapha Hukumar kare hakkkin musulmi ta duniya, wato IHRC ta damu matuka game da makomar masu tattakin arba’in da 'yan s...
Daga Zailani Mustapha
Hukumar kare hakkkin
musulmi ta duniya, wato IHRC ta damu matuka game da makomar masu tattakin arba’in
da 'yan sanda suka kai wa hari ko kuma suka kama su a Nijeriya a yayin da suke
halartar tattakin Arba'in a babban birnin tarayya Abuja.
'Yan sanda sun bude
wuta kan masu tattakin a ranar Lahadi 25 ga Maris 2024 ba tare da gargadi ko an
tsokane su ba a yayin da ake gudanar da tattakin cikin lumana domin nuna
alhinin kan kisan kiyashin da aka yi wa jikan Manzon Allah, Imam Husayn.
Yanzu haka dai an
tabbatar da cewa ‘yan sanda sun kashe masu tattakin guda hudu tare da kai
gawarwakinsu zuwa wani wuri da ba a bayyana ba. Wasu daruruwa kuma sun samu
raunuka ciki har da masu harbin bindiga tare da kama wasu daga cikin masu
raunin a inda aka yi tattakin da kuma wani muhalli da ‘yan sanda suka dira. Har
ila yau, ba a san inda suka kai su ba.
Kwashe su da ‘yan sanda
suka yi wani lamari ne da ke da matukar tayar da hankali duba da irin yadda
‘yan sandan Nijeriya ke dira kan mahalarta tattakin Arba’in a matakin kisan kai.
A yayin gudanar da tarukan na Arba’in a
shekarar 2019 ‘yan sanda sun kwashe gawarwakin wasu masu tattaki guda shida wadanda
suka bindige har lahira, inda suka boye su domin boye laifin kisan kan da suka
yi. Sai a bana ne aka saki wadancan gawarwakin bayan doguwar shari'a da aka
kwashe ana gudanarwa.
Tsaron wadanda aka kama
al’amari ne mai matukar damuwa da tayar da hankali. Domin a shekarar 2019, 'yan
sanda sun kama wasu masu tattaki da suka jikkata daga wani asibiti da suke karbar
magani. Daga baya wasu sun mutu a hannun ‘yan sanda.
Wasu rahotannin a
faifan bidiyo, sun kuma bayyana cewa ‘yan sandan Nijeriya sun cire wa mata
musulmi hijabi da karfi da yaji. An yada hoton bidiyon lamarin a shafukan sada
zumunta. Hakan dai ya janyo cece-kuce a tsakanin musulmin kasar baki daya.
Tattakin Arba’in da ake
yi duk shekara ya zama lamari da jami’an tsaron Nijeriya a ‘yan shekarun nan da
suke kai mata hari, inda ba a wuce shekara guda ba ke nan, ‘yan sanda suka kai
hari kan masu tattakin, lamarin da ya janyo hasarar rayuka.
An shafe shekaru 40 ana
gudanar da Muzaharar Arba'in da Ashura a duk fadin Nijeriya amma a 'yan
kwanakin nan an fuskanci munanan hare-hare yayin da gwamnati ta dauki matakin
murkushe Harkar Musulunci ta Nijeriya da jagoranta da ke shirya irin wannan
tattakin.
No comments