Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Rikicin Beji: An Nemi Makiyaya Da Manoma Da Su Kai Zuciya Nesa

Daga Awwal Umar Kontagora An yi kira ga bangarorin manoma da makiyaya da su kai zuciyarsu nesa, su rungumi zaman lafiya, shi zai kawo masu y...


Daga Awwal Umar Kontagora

An yi kira ga bangarorin manoma da makiyaya da su kai zuciyarsu nesa, su rungumi zaman lafiya, shi zai kawo masu yalwar arziki. Wakilin fulanin minna kuma shugaban kungiyar Bago Ruga-Ruga ta jihar Neja, Alhaji Hassan Usman Shiroro ne ya yi kiran jim kadan janazar dan sa Muhammad Baba ya rikicin ya rutsa da shi akan hanyarsa ta zuwa Kontagora daga Minna.

Marigayi Muhammad Baba shi ne shugaban kamfanin sarrafa shinkafa ta Alhaji Hassan Shiroro, yana kan hanyarsa cikin motar kasuwa inda wasu hasalallu suke tare motocin haya da ke kan tafiya, inda suka fito da shi cikin motar suka kashe shi nan take sakamakon wani rikicin da ya barke sakamakon samun gawar wani manomin da aka tsinci gawarsa a gonarsa.

Rikicin ya lakume rayukan mutane shida, yarinya daya da wasu yan uwan juna su uku da aka iske su har rugarsu aka kashe su, da wani dattijon bafulatani da bai gani da kuma marigayi Muhammad Baba, wanda da ne ga Alhaji Hassan Shiroro mai kamfanin sarrafa shinkafa da ke minna.

Wakilin fulanin, yace wasu batagari ne da ke yiwa zaman lafiya zagon kasa, wanda gwamnatin jiha tuni ta kamo hanyar samar da maslaha ga manoma da makiyayan jihar.

Saboda ya kamata dukkanin bangarori su yi hakuri a rungumi zaman lafiya. Ya kara da cewar jami'an tsaro na bakin kokarin su, dan haka a barsu su yi aikinsu.

Da yake jawabi bayan ganawar sirri da masu ruwa da tsaki da sarakuna a garin na Beji da ke karamar Hukumar Bosso, mataimakin gwamna Neja, kuma mai rikon kujerar gwamna a halin yanzu, Kwamred Yakubu Garba, yace gwamnatin jiha ba za ta bar wannan abin ya wuce haka kawai ba, sun kafa kwamitin bincike kuma duk wanda aka samu da hannu a wannan rikicin ba zai sha ba.

Dan haka ina baiwa dukkanin bangarorin da abin ya shafa da su yi hakuri a zauna lafiya kuma gwamnati za ta tabbatar tayi wani abu akai dan kaucewa faruwar irin wannan a gaba.
Garin Beji na Beji dai, wanda mafi rinjayen mazaunarsa gwarawa da fulani da suka kwashe shekaru suna zaman lafiya da juna, wanda suka shahara wajen kiwo, noma da kasuwanci.

Amma a dan kankanin lokacin nan sakamakon matsalar tsaro da ya addabi yankunan arewa na yaduwar yan ta'addan daji masu garkuwa da mutane dan karban kudin fansa, yasa tsakanin al'ummomin yankin aka koma ana yiwa juna kallon hadarin kaji.

Wakilin Minna, ya ce mu al'ummar fulani masu son zaman lafiya ne, kan haka yasa muka rungumi kudurin gwamnatin Neja hannu biyu kan zaman lafiya da kyautatawa juna, dan haka ina jaddada bukatar kowa yayi hakuri mu barwa Allah lamarin, kuma mu saurari matakan da gwamnatin jiha za ta dauka kan wannan lamarin da ya auku.

No comments