Daga Awwal Umar Kontagora Majalisar gudanarwar Jihar Kebbi ta amince da kafa wani kwamiti na mutane 16 da za su yi aiki akan hanyoyin da za...
Daga Awwal Umar Kontagora
Majalisar gudanarwar Jihar Kebbi ta amince da kafa wani kwamiti na mutane 16 da za su yi aiki akan hanyoyin da za'a magance matsalar afkuwar ambaliyar ruwa a jihar.
Kwamitin zartarwar ta amince da hakan ne a wani zaman da ya gudana ranar laraba da ta gabata a karkashin jagorancin Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris Kauran Gwandu.
Haka kuma sanarwar ta fito ne ta bakin kwamishinan yada labarai da raya al'adu, Alhaji Yakubu Ahmed Birnin Kebbi, yayin da yake wata ganawa da yan jarida jim kadan bayan kammala taron.
Kwamishinan ya kara da cewar gwamnati ta amince da nadin kwamitin ne nan take domin samar da hanyoyin magance matsalolin ambaliyar ruwa da ake fuskanta a wasu kananan hukumomin jihar.
Ya kara da cewar hasashen yanayi ya nuna za'a samu matsalar ambaliyar ruwa a jihar, sannan yace koda yake hasashe ne ba lallai ya zama gaskiya, amma gwamnatin Kebbi ba zata jira sai ya auku ba, dole zata yi kokari gwargwadon hali wajen dakile wannan matsalar domin kuwa mun ga yadda ambaliyar ruwa a bana ya yiwa wasu jihohi a kasar nan.
Kwamishinan ya cigaba cewar hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA ita ma ta bayar da sanarwar samun ambaliyar ruwa wanda zai iya afkuwa daga wajen Nijeriya wanda zai iya shafar wasu sassan jihar Kebbi wanda hakan na daga cikin dalilan da suka sanya gwamnati kafa wannan kwamitin karkashin jagorancin mataimakin gwamna Sanata Umar Abubakar Tafida domin samar da hanyoyin magance wannan matsalar.
Ya kara da cewar suna sane da gargadin da hukumomi suka yi na yi yuwar samun ambaliyar ruwa daga Central Guinea, Futa Jalo Highland region, River Senegal, River Gambia da kuma River Niger wanda aka ce ambaliyar ruwan su zai iya shafar wasu yankuna na kasar nan.
Kwamishinan ya bayyana cewar daga cikin rahoton hasashen da suka samu ya nuna cewar ambaliyar ruwan za ta shafi Jihar Kebbi inda za tafi shafar karamar hukumar mulkin Bunza ta jihar Kebbi.
Kwamitin zai fara aikin sa ranar Alhamis inda zai hadu da shugabannin kananan hukumomin Jihar yayi musu bayani su kuma su yiwa sarakunan gargajiyar yankunan su bayani akan matsalar.
No comments