Daga Awwal Umar Kontagora An bayyana rikicin da yayi sanadiyar lakume rayuka da dukiyoyin jama'a a yankin Barkuta na gundumar Beji a kar...
Daga Awwal Umar Kontagora
An bayyana rikicin da yayi sanadiyar lakume rayuka da dukiyoyin jama'a a yankin Barkuta na gundumar Beji a karamar hukumar Bosso da ya auku a kwanakin baya bai da nasaba da kabilanci ko Fulani makiyaya da Gwarawa manoma. Domin tsakanin su ba gaba kuma babu wani sabani a tsakanin su.
Kwamishinan ma'aikatar kula da jin dadin manoma da makiyaya, Hon. Umar Ahmad Sanda ( Rabe) ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Minna.
Kwamishinan yace rikici ne na daukar doka a hannu wanda ya faru tsakanin yan sa kai, wadanda ma wata kila hukuma ba ta san da zaman su ba, suka aikata wannan mummunar aikin, amma duk wanda yace rikici ne tsakanin Fulani da Gwarawa ne to ba gaskiya ba, domin dukkanin bangarorin nan biyu suna da kyakkyawar fahimtar juna.
Hon. Rabe, cikin ikon Allah bisa wasu matakan da gwamnatin jiha bisa jagorancin mataimakin gwamna, da fadar mai martaba sarkin minna, an kafa kwamiti kuma sun ziyarci yankin dan sanin hakikanin abinda ya faru, wanda da yardar Allah za a dauki kwakkwarar mataki akan wannan lamarin dan gudun faruwar hakan a gaba.
A hukumance za mu bi salsalar faruwar lamarin kuma gwamnati za ta tabbatar hakan bai sake faruwa a gaba in Allah ya yarda.
No comments