Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Samar Da Dunkulalliyar Kasa Shi Ne Buri Na, Inji Sarki Bayero

  *Samar Da Dunkulalliyar Kasa    Shi Ne Buri Na, Inji Sarki Bayero *Tsiraru Ke Kiran Raba kasa Don Muradin kashin Kansu, Sarkin Kan...

 



*Samar Da Dunkulalliyar Kasa   Shi Ne Buri Na, Inji Sarki Bayero

*Tsiraru Ke Kiran Raba kasa Don Muradin kashin Kansu, Sarkin Kano

*Banbancin Da Ke Tsakaninmu Bai Kai Abubuwan Da Suka Hada Mu Ba

Gagarumin bikin mika Sandar Mulki ga Sarkin Kano, ALHAJI AMINU ADO BAYERO, zai wakana a yau a katafaren farfajiyar filin wasanni ta Sani Abacha, kuma a daidai wannan wajen ne marigayin mahaifinsa, Alhaji Ado Bayero ya samu sarautar Sarkin Kano shekaru 53 da suka gabata.

A wannan hirar ta musamman da jaridar LEADERSHIP Weekend ta yi da shi cikin harshen turanci wanda KHALID IDRIS DOYA ya fassara, mai martaba sarkin yi magana kan batutuwan da suka shafi kasa, ciki har da batun kiraye-kirayen raba kasa ko masu neman ballewa, wanda ya ce an samar da wadannan batutuwan ne kawai bisa son zuciya da son kai na wasu kalilan don manufarsu ta daban. Ya kuma yi magana kan sauyin da ya samu a rayuwarsa daga dan Sarki zuwa hadewa kan karagar mulkin Sarki da ya nuna hakan a matsayin abun da ya zo masa da sauki matuka. Ga hirar:

Mai Martaba, ya ka tsinci kanka daga sauyi Yarima zuwa Sarki?

Ka ce sauyi ba zan ce na yarda ko ban yarda ba. Maganar gaskiya ita ce ni an haifeni a cikin wannan tsarin na sarauta; na kuma taso cikin tsari; kama-kama na girma dukka a cikin tsarin. Don haka ba wani abu ne sabo a garen ba.

Abun da ya zama sabo kawai shi ne zama a kujerar Kakannina. Ba lamari ne mai sauki ba, musamman idan aka yi la’akari da halin da ake ciki a yanzu, a matsayinka na shugaba kuma jagora idan lamari ya kasance mawuyaci ga jama’anka kai ne mai daukan nauyin wannan batun.

Kai ne za ka dauki nauyin a kanka. A zahirance zan iya cewa wannan shi ne babban kalubalen da nake fuskanta.

Watakila a lokacin da nake matsayin saurayin mutum ko na ce a lokacin da nake rike da sauratar da ke da wani iyaka a cikin al’umma, to amma yanzu komai ya faru za ka ji shi, don haka sauyin ya zo min cikin sauki da saukka saboda na kasance a cikin tsarin tun usuli wanda na taso a hakan kuma na koyi abubuwa da daman gaske tun kafin yau.

Tun 1990 na kasance cikin lamarin ita kanta. Don haka gabaki daya sai mu ce mun gode wa Allah tare da addu’ar ya cigaba da taimakonmu da agaza mana.

Kasancewarka wanda ka taso a cikin tsarin sarauta, shin ka taba tsammanin za ka zama Sarki wata rana?

Duk wanda dai ya fito daga cikin gidan Sarauta fatansa shi ne wata rana ya zama ya gaji iyayensa da Kakakinsa ya zama shi ne shugaba na mai jan gaba.

Amma ba lamari ne a-yi-ko-a-mutu ba. Abu ne da aka rigaya aka kaddara.

Babban Yayanku zai iya zama Sarki; karamin dan uwanka zai iya zama Sarki; hatta ma danka zai iya zama Sarki. Don haka, fata ne kuma addu’a ne ga duk dan gidan sarauta na wata rana zai iya zama Sarki idan har Allah ya amince masa kuma ya kaddara masa hakan cikin rayuwarsa to la-shakka sai ya zama Sarkin nan wani lokaci.

Gaba daya dai, ba zan ce na yi mamaki ba amma abu guda da zan ce shi ne Allah ne ya maidani abun da na zama a yau. Na zama Sarki ba wai don na fi kowa ba ne, ba wai don na fi kowa arziki da dukiya bane.

Allah ne ya kaddara ya kuma maidani zuwa Sarki. Ina cike da godiya ga ni’imar Allah kan wannan kuma fatana da rokona zai cigaba da agaza mana da taimakona wajen tafiyar da wannan nauyin da ke kaina.

Gwamnan Jihar Kano, a yayin gabatar maka wasikar nadinka kai da saura a matsayin sabbin Sarakuna a shekarar da ta gabata, ya ce kai da dan uwan Sarkin Bichi, kun zama a tarihi ku ne na farko a Nijeriya ko Afrika da aka fara nadawa a matsayin Sarakuna masu daraja ta daya a lokaci guda kuma a jiha. Ya ce, wannan ya faru ne sakamakon nagartaccen aikin da marigayin mahaifinku wanda ya zama sarki na tsawon shekara 53 ya gudanar, Marigayi Alhaji Ado Bayero, hakan kuma bai rasa nasaba da la’ari da kyakkyawar jagoranci da tarihi na kwarai da ya kafa ba.

 

Ta yaya kake yunkurin daurawa daga irin salon da mahaifinka ya tsaya na kafa tarihin kwarai?

Gaba daya dai, lokacin da kake magana kan jagoranci da yadda nake kallo, duk ya shafi meye gadon da ka gada ni kuma ina kan aiki ne kan ababen da na gada daga wajen marigayi Sarki tun 1990 har zuwa 2014 lokacin da ya rigamu gidan gaskiya (Allah Jikansa).

Ina godiya wa Allah domin na samu damar rayuwa mai tsawo da shi wanda na koyi abubuwa daban-daban da suke taimakona da da kuma yanzu. kokarin kwatanta kanmu da marigayi Sarki abu ne mai wuya, amma kallon tsarinsu da salonsu wajen tafiyarwa da harkokin mulki zai taimaka mana sosai wajen kyautata shugabanci na kwarai.

Don haka, ina ganin babban kalubale a gabana amma niyya ta kwarai zai taimaka tare da goyon bayan jama’a, musamman ‘yan majalisata, sauran hakimai, masu rike da sarautu, gwamnati, ‘yan kasuwa, malamai da jama’a, ina tunanin da goyon bayan za mu samu nasarar kafa tarihin kwarai da jama’a za su jima suna tunawa da mu.

Masautar Kano tana da dadadden tarihi, tsohowar masarauta mai girman mulki kuma duk da sauyin zamani har yanzu tana nan da karfin ikonta daram.

Mene ne sirrin?

Sirrin shine gaskata abun da muka yi amannar shine daidai. Al’ada da al’adu, kamar yadda kuka ce, bangare ne na rayuwa muddin kuka rasa al’adarku da al’adunku, babu inda za ku dosa a rayuwa.

A kowani lokaci na kan kasance cikin farin ciki da annashuwa idan na ga matasanmu sun rungumi al’adarsu sosai, don ana cewa, ‘Komai ka gani a rayuwar matasa sannu a hankali ba zai taba bacewa ba’.

Na yi amannar mutane sun rungumi al’ada tun da farko, mutane sun yi amanna da al’adu; sun kuma gamsu da al’adu suna kuma mutuntawa.

Wannan hanyar, aikin rike al’adu na nan ana kai. Abu kawai da kuke da bukata shine a samu wani da zai jagoranci gina al’ada da al’adun jama’arsa, tare da gadon iyaye da kakanni kan abubuwan da suka tafi suka bari.

 

Wannan shine nake ganin iyaye da kakanni sun yi tsawon shekarun da suka kasance masu sadaukarwa wajen rike al’adu da wanzar da su tare da ganin an tabbatar da bunkasa al’adu. Wannan ya taimaka mana sosai ya kuma taimaka wa jama’anmu da mabiyanmu sun kuma gamsu da hakan, muma za mu kara azama da himma a wannan fanni domin daukaka darajar masarautar Kano da al’ummarmu.

Mai Martaba, daga lokacin da ka hau kujerar Kakaninka zuwa yau, masarautar Kano, ta bunkasa, fadar jihar ta samu nasarori wajen gudanar da nargartattun ayyuka. Wasu abubuwa ne kuka kawo domin bunkasa masarautar Kano?

 

To, idan kuna magana kan jagorancin masarauta, muna magana ne a kan daurawa bisa tafarkin iyaye da kakanni da kuma yin ayyukan da za su bunkasa ababen da suka bar mana.

Ina tsammanin a bayyana wannan shine asalin dalilin nasarata. Kamar yadda nake cewa ina cikin tsarin sarauta sama da shekaru 30 da suka wuce kuma wadanda ban hadu da su ba lokacin da suke mulki na karanci tarihinsu kuma na koyi yadda suka tafiyar da masarautar da yadda suka sanya komai a muhallinsa da ya kai ga basu nasarorin da suka cimma inganta jihar da ma kasa baki daya. Don haka, ina mai cikin farin ciki da aka nadani ina mai karamin shekaru.

Aiki tare da marigayi sarki na tsawon shekara 24 ko makamancin hakan ya taimaka min sosai wajen tafiyar da ragamar mulki da kuma gabatar da ababen da na koya daga wajen marigayi Sarki, Abdullahi Bayero, marigayi Sarki Sanusi, tsohon sarkin da na yi aiki a karkashinsa, dukkaninsu sun taimaka min wajen yin ayyukan da nake yi a yau, kuma abu mai gayar muhimmanci shine yadda Allah ya azurtani da hazikan mambobin majalisar Sarki.

Mun kasance masu hada kai waje guda domin fito da ababen da za su taimaka wa al’ummarmu. Suna ba ni muhimman kuma nagartattun shawarorin da suka dace ina neman karin hakan domin cigaba da gudanar da ayyuka na kwarai don al’ummar mu.

Akwai kiranye-kiranyen da aka yi ta yi na raba kasa ko ballewar wasu sassan kasa. A matsayinka na Basarake wanda ke da dumbin sani kan tarihin kasa kana da kake kula da al’adun mutane mabanbanta, menene kake tunanin ya janyo irin wannan batun ballewar wasu gungu daga kasar kuma me hakan zai iya janyo wa kasar?

Kamar yadda na fada ma abokan aikinku da farko, idan ka zauna da wani da ya fito daga yankin Kudu ko Arewa kuka yi magana kan dukkanin batutuwan sake fasalta kasa, abun da zai fada maka zai sha banban da abun da wani mutum din ma zai fada maka da suka fito daga yanki guda.

Kamar ma dai akwai rashin fahimta a tsakanin wadanda suke ganin sun yi zurfi kan wannan bukatar, kawai abun da ke akwai ra’ayoyi ne na wasu mutane kalilan da suke son kare muradinsu da son ransu, batu ne na muradin kashin kai.

Don haka, bari mu kalli wadanda suka yi sadaukar suka yi hidima da ake kiransu masu ruwa da tsakin da suka zage damtsensu har Nijeriya ta kawo inda take a yau. Su zo su hada kansu su duba, ‘yan banbance-banbancen da suke akwai kalilan ne idan aka kwatanta da abubuwan da na yi imanin sun hada a tarayya.

Sannan, na yi amannar dukkaninmu, masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnonin jihohi, Sarakuna, da sauran sassan al’umma, za mu iya hada kanmu waje guda da tsarkakekken zuciya, tabbas da za mu iya fito da mafita kan dukkanin ‘yan matsalolin da suke akwai. Kamar yadda na ce ne, yadda kuka ga na rungumi kowa da kowa wani bari ne na gudunmawar da zan iya bayarwa wajen hada da dunkulewa gami da tabbatar da Nijeriya ta yi nasara, dukkanin Sarakunan da na gana da su, dukkanin gwamnonin da na hadu da su, dukkanin masu ruwa da tsakin da na hadu da su a wajen taro sun bayyana min ra’ayinsu kan batun wargaza kasa.

Don haka ina da tabbacin wasu ‘yan kadan kuma kalilan ke wannan yekuwar kuma ba don komai suke hakan ba illa don ra’ayinsu na kashin kai, ina da imanin cewa mu zauna gaba daya mu tattauna kan matsalolinmu, mu ayyano su mu fito da su don yin aiki tare wajen tabbatar da cigaban kasa da al’ummarta.

A matakin da ake cigaba da fuskantar matsalar tsaro, yawaitar kashe-kashe, garkuwa da mutane, Jihar Kano ta kasance mai cin gajiyar zaman lafiya a irin wannan lokacin.

Mene ne aka yi na daban a nan ko gudunmawar Sarakuna da aka samu wannan nasarar?

 

Ina tsammanin kowa zai so yin abun da Kano take yi domin hakan zai iya sanya su cikin farin ciki. Abu mai gayar muhimmanci a nan shine muna da jajirtattun shugabanni.

Muna da gwamnati mai kula da sha’anin tsaron jihar sosai. Ba wai sauran jihohin ma basu maida hankali wajen amfani da dukiyarsu domin kula da sha’anin tsaron jihohin bane, amma Gwamnan Kano yana kokarinsa sosai.

Sauran bangarorin jama’a, da suka kunshi limamai, fastoci, sarakuna, al’umma kowa na bada nasa gudunmawar musamman addu’o’in da ake yawan yi domin wanzuwar zaman lafiyar jihar. Ina tunanin Allah ya amsa mana addu’o’inmu, ba wai Kano ce kawai muke mata addu’a ba. Muna addu’a wa sauran jihohinmu da kasar ma baki daya.

Don haka ina kira ga kowa da kowa a cikin al’umma da ya shigo a dama da shi wajen yaki da matsalar tsaro domin lamarin ya shafi kowa da kowa. kowa da kowa ya fito ya bada nashi gudunmawar ta addu’a, shawarwari, gabatar da tunaninsa na yadda za a hada kai waje guda domin ganin an fito da hanyoyin shawo kan wannan matsalar na btun rashin tsaro da ke akwai.

Abun takaici ne ka ga mutanen da suka zauna tare tsawon sama da shekaru 60 amma sun dawo suna gaba da juna sun zama abokan gaba.

Meye jawo hakan?

Dole akwai wani dalilin da ya jawo kuma ina tunanin zama tare domin duba muhimman batutuwa da suke faruwa tabbas ta hakan matsalolinmu da daman gaske za su kai ga zama tarihi sannu a hankali.

A lokacin ziyararka zuwa Jihar Oyo, Alaafin na Oyo, Oba Lamidi Adeyemi, ya ce, shi da marigayi mahaifinka, sun daga wa gwamnatin tarayya jijiyar wuya tare da tabbatar da Sarakunan Gargajiya sun fara cin gajiyar kaso biyar daga cikin kudaden da ake ware wa kananan hukumomin da suke yankunansu.

A yanzu batun samar wa Sarakunan aikin yi a tsarin mulkin har yanzu bai tabbata ba. Kana ganin akwai bukatar a fayyace wani aikin da za a baiwa Sarakunan a hukumance da zai kasance daga kundin tsarin mulki?

Ina tunanin zan yi magana kan ra’ayina na kashin kai. Abu mai muhimmanci mutum kamar Alaafin na Oyo yana nan; marigayi mahaifina da yake Sarauta sama da shekara hamsin tare da sauran Sarakunan da suka shafe shekaru da dama.

Idan suka ce akwai bukatar samar da aikin yi wa Sarakuna a hukumance ni waye da zan ce a’a ko na ja?

Ni zan yi amanna da abun da suka gamsu da shi. Babu wani dalilin da zan yi tunanin da ya saba da nasu a lokaci guda kuma na gamsu da cewa gudunmawar da sarakuan gargajiya ke bayarwa kula da al’umma tare da cewa aikin kula da al’umma da jagorantarsu ma babban aiki ne da ya ishi Basarake, don haka mu cigaba da aiki domin bunkasa hakan, amma ina son na ce idan mafiya suka raja’a a kai da manyan magabatana ban da wani dalili na kin amincewa.

Kwanakin baya ka jagoranci gangamin wayar da kai kan ilimin ‘ya’ya Mata. Ta yaya kake ganin Nijeriya da Arewa ya dace su fi maida hankali, don ganin an shawo kan wannan matsalar na ilimin ‘ya’ya mata da kuma yawaitan yara Mata da basu zuwa makaranta?

Batun ilimin ‘ya’ya Mata da ma ilimi gaba daya abu ne mai gayar muhimmanci da yake neman a maida hankali sosai a kai.

Idan kuka kalli al’umma komai lalace; al’umma gabaki daya, daga gwamnati, sarakuna zuwa malamai, da ‘yan kasuwa, ma’aikatan gwamnati tare da daidakun jama’a.

Abubuwa dai basu tafi yadda ya dace amma idan muka hada kawukanmu guda komai zai saukaka, fannonin jama’a kowa ya fito a kula da fannin ilimin yara mata.

Kamar yadda na sha fadi ne, ilimin ‘ya’ya mata na da matukar alfanu ga al’ummarmu saboda ilmantar da diya mace kamar ka ilmantar da al’umma baki daya ne. don haka dukkanin wani abun da muke tunanin za mu iya bada gudunmawarsa don bunkasa ilimin nan lallai ya dace dukkaninmu mu yi.

A kan hakan mun zauna da kungiyoyi da dama muka gana da su kan ilimin yara mata. Ina da mambar majalisarta da ke shugabanta sashin, muna aiki tare da masu ruwa da tsaki domin ganin yadda za a yi a bunkasa ilimi tare da magance matsalolin da suke akwai a wananin fannin.

 

Muna hada kanmu da gwamnatoci, kungiyoyi dban-daban na kasa da kasa da na cikin gida domin yadda za a yi a bullo wa wannan matsalar.

Sannu a hankali kuma muna kan lalubo bakin zaren magance matsalolin don haka za mu cigaba da tsage damtse wajen ganin ilimi ya inganta.

Ta yaya zaka sanya gwamnatin jihar ta tabbatar da samar da ayyukan yi ga matasan da basu da aikin yi a jihar Kano?

Kamar yadda na jima ina fadi, matsalar rashin aikin yi ba kawai a jihar Kano ne ya yi katutu ba; ba kuma ya mamaye Arewacin kasa bane zalla, kodayake an fi kurara batun a nan.

Dukkanin abun da ke akwai, wadannan kalubalen idan aka hadasu waje guda matsaloli da suke addabar duniya baki daya. Tattalin arziki ya yi kasa; mutane na ta kokarin tunanin yadda za a samar da mafita kan wannan matsalar da ke addabarmu.

Na yi magana da gwamnati kusan kullum kan wannan batun, ba abu ne da a kowani lokaci zai fito ina cewa na yi magana a kai ba, amma lallai kusan kullum muna fada wa gwamanti wannan matsalar.

Na san matsayina na Sarki wanda a kowani lokaci nake iya fada wa gwamnati bukatun jama’ata.

Zan cigaba da yin duk mai yiyuwa wajen magana da su a kowani lokaci, basu shawarwarin da suka dace na kuma tabbatar gwamnati za ta ke saurara tare da daukan matakan da suka dace a kai.

Idan muka yi nazarin halin da tattalin arzikinmu ke ciki, za mu ga yadda za mu jawo ra’ayin masu hannu da shuni da su taimaka wa kokarin gwamnati wajen ganin an fita daga wannan matsalar na rashin aiki yi a tsakanin jama’anmu.


Daga Jaridar Leadership A Yau


No comments