Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Bakwai Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

  Gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana cewar ‘yan bindigar dake garkuwa da mutane a jihar sun hallaka mutum bakwai da suka kama a kananan hukum...

 


Gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana cewar ‘yan bindigar dake garkuwa da mutane a jihar sun hallaka mutum bakwai da suka kama a kananan hukumomin Chikun da Kajuru da kuma Giwa.

Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Samuel Aruwan ne ya bayyana haka sakamakon rahotannin da ya samu daga hukumomin tsaron jihar.

Aruwan ya ce rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun kashe mutane 4 da suka kama a kusa da Tsohon Gayan dake karamar hukumar Chikun, yayin da 2 daga cikin su suka fito daga kauyen Kakau, guda kuma ya fito daga Kachia sai kuma na 4 da ba a iya tantancewa ba.

Sanarwar kwamishinan ta ce an kashe kuma mutane 2 a Tashar Iri dake karamar hukumar Kajuru, sai kuma guda a tsohon Farakwai dake Igabi.

Aruwan ya ce Gwamna Nasir El Rufai ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda aka kashe.


No comments