Rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar kashe ‘yan bindiga 624, sannan ta kama wasu 151, ciki har da masu taimaka wa ‘yan ta’adda da a...
Rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar kashe ‘yan bindiga 624, sannan ta kama wasu 151, ciki har da masu taimaka wa ‘yan ta’adda da aka fi sani da infoma, cikin watan Mayun da ke dab da Æ™arewa.
Sojojin sun kuma ce sun ceto kimanin mutum 563 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a cikin watan.
Rundunar sojojin ta kuma ce ta nuna damuwa game da kisan wasu jami’anta sha bakwai da aka yi a jihar Delta watannin baya da kuma wani jami’inta da wasu ‘yan ta’adda suka yi a babban kantin sayar da kaya na Banex Plaza da aka yi a kwanan nan, sai dai ta ce ba abinda za ta ci gaba da lamunta ba ne.
Mai magana da yawun kakakin rundunar sojin Æ™asar, Manjo Janar Edward, wato Captain Ibrahim Bukar Ali ya shaida wa BBC cewa yaÆ™i da ta’addanci na neman goyon bayan al’umma tare da samun cikakken haÉ—in kai da yarda tsakanin jami’an tsaro da fararen hula, kasancewar suna buÆ™atar jami’an tsaro a tare da su domin tsaron rayukansu da ma dukiya.
Ya Æ™ara da cwa sojojin Æ™asar za su ci gaba da yaÆ™ar ‘yan ta’adda har sai sun samu cikakkiyar nasara a kansu
Kaftin Ibrahim Ali, ya ce rundunar sojin ta kuma samu manyan nasarori da suka haɗa da ƙwace makamai da dama da suka haɗa da bindiga kirar AK 47 411, da kuma harsasai 16,487.
Kazalika rundunar ta ce ta ƙwace ɗanyen mai da kuɗinsa ya kai naira miliyan 705,836 a yankin kudancin ƙasar.
No comments