Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Dakta Hassan Gimba A Mahangar Hankali

Daga Idris Umar, Zariya Dakta Hasan Gimba mawallafi jaridar yanar gizo mai suna NEPTUNE PRIME dake babban birnin tarayya Abuja. A mahangar...



Daga Idris Umar, Zariya

Dakta Hasan Gimba mawallafi jaridar yanar gizo mai suna NEPTUNE PRIME dake babban birnin tarayya Abuja. A mahangar hankali kafin ka yabi mutum ka je kusa da shi ko ka zauna kusa da shi za ka gane ko wane ne shi.

Haka zalika idan kana so ka gane mutum ko shi wane ne ka barshi ya yi magana tukunna daga nan zaka gane wane ne shi. Ba kasafai na kan ware lokaci na yi rubutu akan wani ba amma ance yabon gwani ya zama dole kuma ko da naka kakan so na kwarai.

Dakta Hasan Gimba mawallafin jaridar NEPTUNE PRIME mutum ne mai kishi harkar yaÉ—a labarai, mai son ci gaban gidajen jaridu gida da waje matukar ya hangi adalci a cikin tafiyar.

Bari na yi amfani da wannan lokaci wato lokacin da mawallafi ke gudanar da ziyara tare da yin addu'a a muhallin da  iyayensa ke kwance wato makabartar NEPA dake garin Potiskum ta jihar Yobe.

Cikin alhini muna roko tare da fatan Allah ya Æ™arbi ziyarar tashi da dukkan addu’o’in da ya yi wa iyaye nasa a lokaci baya da kuma daidai wannan lokacin.

Wato yin amfani da wannan lokacin ne zai sa jama’ar da muke tare da su na nesa da na kusa su fahimci abin da nake nufi ga hazikin mawallafin kuma abokin tafiya ga duk wani dan jarida a kasarmu da duniya baki daya.

Dakta Hassan Gimba ya zama na gaba-gaba a wajen janyo hankalin gwamnati tarayya da gwamnatin jihohi da Æ™ananan hukumomi a duk lokacin da ya hango suna Æ™oÆ™arin tafka kuskure a kowanne É“angare musamman wuraren da suka zama Æ™ashin bayan mulkin jama’a kamar harkar lafiya da harkar Ilmi da abin da ya shafi tsaro da dai sauransu.

Dakta Hasan yana daga cikin mutanen da ake girmamawa a arewa da kudu a É“angaren hasashen da bayar da shawara a jaridance kuma a hukumance. Kuma an shaidi kafar yaÉ—a labaransa wato Neptune Prime da Æ™okarin kare mutuncin al’ummar Æ™asa baki daya.

Dakta Hassan Gimba mutum ne da ko wani yaro zai so ya zama ubansa kuma ko wani dattijo zai so ya zamo ɗansa a ɓangaren zamantakewar juna. Mun shaide shi da kare mutuncin kansa wajen kaucewa yin karya a cikin harkokinsa babu cin amana kuma.

Gimba mutum ne mai dauriyar a lokacin da ba yi da shi kuma samun sa baya sashi girman kai  ga naÆ™asa da shi. Bisa haka ne muke wa kasarmu addu’a Allah ya yawaita irinsu Dakta Hassan Gimba domin aikin alheri su Æ™aru a ko’ina a faÉ—in Æ™asa.

Farko bayan gaisuwa na girmamawa zanyi ta’aziyya na rashin da aka yi masa na rasuwar Alhaji Gimba Ahmad (Baba) wanda mahaifi ne gare shi da Hajiya Hafsatu Gimba Ahmad (Mama) wacce mahaifiya ce gare shi, sai matarsa Hajiya Fatimah Balarabe, Allah ya gafarta masu baki É—aya.

Wani abin ban sha’awa ga mawallafin jaridar ta Neptune Prime dake Abuja wato Dakta Hasan Gimba, mutum ne haziki mai hangen nesa shiyasa ma da yawan ma’aikatansa ke masa lakabi da Babanmu.

Alhaji Hasan Gimba mutum ne mai tausayin al’umma yana jan kowa a jika don sanin me ke damun sa don bayar da taimako a gare shi.

Dan binciken da muka yi ya nuna Gimba yana bacci ne Æ™alilan domin da yawan harkokinsa nazarce nazarce ne kawai kuma wani abin ban sha’awa shi ne yana bayar da hankalinsa ne a É“angaren wayar da kan al’umma ba don neman abin duniya ba amma in ya samu ya kan nuna godiya ga Allah don zai yi kyauta har da sadaka ga jama'ar da yake tare da su.

Dakta  Hassan Gimba ya gaji mahaifinsa ne Alhaji Gimba Ahmad wajen yima al’umma hidima. Mahaifin Dakta Hasan Gimba wato Alhaji Gimba Ahmed shima ya yi fice a wajen taimakon al’umma da Æ™wantar da hankalin jama’ar dake zaune kusa da shi.

Shiyasa ma a lokacin rasuwar mahaifin nasa duk wani babban mutum dake  jihar Yobe sai da ya girgiza da rasuwar Alhaji Gimba Ahmad. Al’ummar jihar Yobe sun yi kukan rashin Alhaji Gimba Ahmad a cikinsu. Amma abin da Allah ya tsara babu yadda za a yi sai ya faru Allah ya sanyaya maÆ™wancin Alhaji Gimba Ahmad yasa Aljanna makomarsa.

Maganar da manya kan faɗa cewa duk idan kagga Gwarzon namiji to akwai jarumai mace kusa da shi wannan lamarin haka yake domin Dakta Hasan Gimba ya gado wasu kyawawan ɗabi'un ne daga wajan mahaifiyarsa musamman halin nan nasa na son taimakawa na ƙasa da shi wanda suka san mahaifiyar Dakta Hassan Gimba wato Hajiya Hafsatu Gimba Ahmad, sun yi mata kyakkyawar shaida wajen son mutane kuma an tabbatar abin hannunta bai taba rufe mata idanu ba. Tana da tausayi sosai ta kuma taimakawa maigidanta Alhaji Gimba Ahmad a ɓangaren kyautata alaƙarsa da mutanen garin Potiskum da jihar Yobe baki daya. Allah ya kai haske ga kabarinsu baki daya.

Hajiya Lami Fatima Balarabe ita ce matar Dakta Hasan Gimba wanda Allah ya yi mata rasuwa babu daɗewa. Hajiya Lami Fatima kallabi tsakanin rawuna, mace kamar maza kafin komawa ta ga Allah ta bar tarihi masu yawa a ɓangaren kula da maigidanta da danginsa da abokan zamanta da abokan arziki da suke tare da shi. Allah ya jiƙanki da rahamarsa.

Hajiya Lami ta koma ga Allah a hannun maigidanta Dakta Hasan Gimba wanda  mutane dubbai ne suka yi masa jaje a yayin da ya sanar da rasuwar ta a shafinsa na sada zumunta wanda hakan ke nuna cewa Hajiya Lami ta koma ga Allah yayin da ake kaunar ta wanda hakan  alama ce ta samun rahama.

Hajiya Lami Fatima har yanzu al’umma na jin daÉ—in ababen alherin da kika kafa a zuciyar mijinki. Bisa haka ne muke rokon Allah ya kai rahama gareki da sauran iyayen mu da suka rigamu gidan gaskiya.

 

Idris Umar ya rubuta, za a iya samunsa a adireshin imel kamar haka: idrisu081@gmail.com

No comments