Wasu tsofaffin kwamishinonin tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i, sun zargi Majalisar Dokokin jihar da shaci fadi, cikin r...
Wasu tsofaffin kwamishinonin tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i, sun zargi Majalisar Dokokin jihar da shaci fadi, cikin rahoton da ta fita na zargin tsohon gwamnan jihar da handame dukiyar al'umma.
Tsaffin kwamishinonin sun ce an yi hakan ne da gayya, kana aka ƙi ba su damar bayyana a gaban kwamitin da aka kafa domin gudanar da wannan bincike domin su fayyace komi, a maimakon hakan ma sai aka tsaurara ƙa'idojin da aka sanya.
Ɗaya daga cikinsu Já’afaru Sani, ya faɗawa BBC cewa wasu daga cikin basussukan da rohoton ya ce sun karɓo shifcin gizo ne, ba a karɓa ba, kuma basu shiga asusun gwamnatin jihar Kaduna a zamanin mai gidan na su ba.
Ya ce "Basussuka da ake magana mun karɓo na kasashen waje mun ga kusan guda biyar, a ciki akwai na dala miliyan 280 don gina hanyoyi a karkara, bamu karɓi wannan ba, akwai kuma wani na dala miliyan150 na aikin gona a wani wuri na musamman, shima ko sisi ba a saka a asusun gwamnati ba'' Inji Jafaru Sani.
Har Ila yau, ya ce "Akwai wani bashi da kwamitin majalisar ya ambato na dala miliyan 130 da wata dala miliyan ɗari bakwai na mayar da yara da ke gararanba a tituna zuwa makaranta, sai wani na dala miliyan 20 da aka shirya amfani da su kan yadda za a farfaɗo da kiwon dabobi, dukkansu ba a ƙarbo su ba kuma babu ɗaya daga cikinsu da ya shiga asusun gwamnati"
Ya bayyana cewa jami'ar tsohuwar gwamnatin da ta gabata ba sa fargabar amsa gayyatar EFCC don ba da ba'asi.
No comments