Daga Awwal Umar Kontagora Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar yayi kira ga yan siyasar jihar Sokoto da su yi koyi da yan s...
Daga Awwal Umar Kontagora
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar yayi kira ga yan siyasar jihar Sokoto da su yi koyi da yan siyasar jihar Kebbi, Sarkin musulmi yayi wannan kiran ne ganin yadda ya ga tsoffin gwamnonin jihar Kebbi suka zauna kusa da juna har da gwamna ma ici cikin farin ciki da raha da juna a lokacin bukin al'adun gargajiya na masarautar Gwandu.
Sarkin Musulmi ya bayyana jin daÉ—insa akan hakan inda yayi kira da za'a a samu irin wannan haÉ—in kai da siyasa mai tsafta irin wannan da ya gani ga shugabannin siyasar jihar Kebbi.
Sarkin Musulmin ya bayyana wannan haɗin kai da ya gani tsakanin tsoffin gwamnonin Kebbi a matsayin abin koyi kuma abin alfahari inda yace duk da banbancin siyasa ko jam'iyya bai hana gwamnoni haɗuwa wurin ɗaya ba domin cigaban al'ummar Jiharsu da kuma haɓaka irin kokarin Malam Abdullahi Fodiyo a jihar da yayi a baya.
Sa'ad Abubakar yayi wannan kiran ne a garin Birnin Kebbi a lokacin gabatar da wata ƙasida akan rayuwar Malam Abdullahi Fodiyo da aka gudanar a masaukin shugaban ƙasa da ke garin Birnin Kebbi a wani ɓangare na bikin wasan al'adun gargajiyar masarautar Gwandu.
No comments