Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

“Yarjejeniyar kisan kai da Isra’ila”: Harkar Musulunci ta Soki Gwamnatin Tarayya Kan Sabuwar Kawancen Tsaro Da Isra’ila

  Daga Zainab Rauf, Abuja  Harkar Musulunci a Nijeriya a karkashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky ta yi kakkausar suka ga sabuwar yarjej...

 

Daga Zainab Rauf, Abuja 

Harkar Musulunci a Nijeriya a karkashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky ta yi kakkausar suka ga sabuwar yarjejeniyar hadin gwiwar tsaro da tattalin arziki da aka kulla tsakanin gwamnatin Nijeriya da kasar Isra’ila, tana kiran wannan mataki a matsayin cin amana ga al’ummar Falasɗinu da kuma “mummunar kawance” da abin da ta kira da “gwamnatin kisan kare dangi.”

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar, 23 ga Agusta, wacce Sidi Munir Sokoto ya sa wa hannu a madadinta, Harkar Musulunci ta bayyana bacin ranta kan wannan yarjejeniya wacce aka cimma tsakanin Ministar Harkokin Waje ta Nijeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, da abokiyar aikinta ta Isra’ila, Sharren Haskel-Harpaz.

Harkar Musuluncin ta zargi Isra’ila da aikata laifukan yaki a Gaza, tare da sukar gwamnatin Nijeriya saboda shiga huldar diflomasiyya da tattalin arziki da wata kasa da take fuskantar shari’a a Kotun Duniya (ICJ) kan laifin kisan kare dangi, wariyar launin fata da laifukan cin zarafin ɗan adam.

“Wannan ba kawai cin amana ba ne — hadin kai ne da masu kisa, kuma zunubi ne marar yafuwa ga bil’adama,” in ji sanarwar. “A daidai lokacin da aka kashe sama da mutane 60,000 a Gaza tun watan Oktoba 2023 — ciki har da mata, yara, tsofaffi da Kiristoci — gwamnatin Nijeriya ta bude kofa ga wadannan masu zubar da jini ba tare da jin kunya ba.”

Harkar ta tunatar da wasu jawabai da jami’an gwamnati suka taba yi a baya, suna sukar yadda Isra’ila ke tafiyar da al’amuran Gaza. A watan Maris 2024, Ministan Harkokin Waje Yusuf Tuggar ya bayyana halin da ake ciki a Gaza da cewa “ya fi karfin lissafi kuma abin kunya ne.” Haka nan, Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima a jawabinsa a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79, ya bayyana goyon baya ga ‘yancin Falasɗinu tare da yin tir da kisan kare dangi a Gaza.

Harkar Musulunci ta yi tambaya kan dalilin da ya sa gwamnatin Nijeriya ke canza matsayinta na baya, tana zargin cewa wannan sabuwar yarjejeniya ta saba wa matsayinta na baya. “Ta yaya wannan gwamnati da ke sukar laifuka, amma kuma ita ce yanzu ke sa hannu a yarjejeniya da masu aikata laifukan?” sanarwar ta tambaya. “Wannan ba manufofin wajenmu ba ne — rushe dabi’unmu ne.”

Sanarwar ta kara da cewa, muradun Isra’ila a Nijeriya ba na samar da zaman lafiya ko tsaro ba ne, sai dai neman amfani da tattalin arziki da tsarin leken asiri na kasar don fadada tasirinta a nahiyar Afirka.

Harkar Musulunci ta jaddada kin amincewarta da duk wata alaka da Isra’ila a Nijeriya, tana kira ga ‘yan Nijeriya masu addinai daban-daban da su ki amincewa da abin da ta kira “kawance da masu kisa.”

“Gwamnatin Nijeriya ta sayar da mutuncinta. Ta ci amanar Falasɗinu kuma ta tozarta al’ummar Nijeriya,” in ji sanarwar.

Har yanzu Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da korafe-korafen da Harkar Musulunci ta gabatar.

 

No comments