Daga Aqil Abdulqadir GABATAR DA HAƘURI GA SARKIN ZAZZAU Da ranar ranar Laraba tawaga na wakilicin Ƙungiyar Jama'atu Izalat...
Daga Aqil Abdulqadir
GABATAR DA HAƘURI GA SARKIN ZAZZAU
Da ranar ranar Laraba tawaga na wakilicin Ƙungiyar Jama'atu Izalatul Bidi'ah Wa Ikamatus Sunnah (JIBWIS) reshen Zariya suka gabatar da ziyarar ban hakuri zuwa Fadan Mai Martaba Sarkin Zazzau.
Tawagan dai ta gabatar da hakuri ga Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, CFR da Majalisarsa bisa Kazafin da 'Daya daga cikin Malaman Kungiyar (Malam Salihu Murtala) yayi ga Mai Martaba Sarkin Zazzau ta kafan Sadarwan Zamani (Social Media).
A lokacin da yake mayar da jawabi, Mai Martaba Sarkin Zazzau wanda tun kafin zuwan wannan tawaga ya yafe ma wanda yayi masa wannan kazafi, yayi kira ga al'umma da su dinga bincike gami da neman bayani bisa kan al'amurra kafin su yada ku kuma su bayyana ma mabiyansu domin gudun tashin hankali da samun dauwawammen zaman lafiya a cikin al'umma.
No comments