Daga Muhammad Farouk A wani yunkurin kawo karshen ta’addanci da matsalar tsaro da ya ki ci ya ki cinyewa a Nijeriya, kwamitin tsaro n...
Daga Muhammad Farouk
A wani yunkurin kawo karshen ta’addanci
da matsalar tsaro da ya ki ci ya ki cinyewa a Nijeriya, kwamitin tsaro na
majalisar Nijeriya da Babban Sufeton 'yan sandan Nijeriya sun bayyana cewa sun samar
da alakar aiki tsakanin sojoji da 'yan sandan kasar wanda hakan zai kara musu
kwarin guiwa da taimaka musu wajen murkushe matsalar tsaron da ake fama da ita a kasarnan.
Rundunar sojin ta bayyana hakan ne a
sanarwar da Kakakinta, Birgediya Janar Mohammed Yerima ya fitar dangane da
ziyara ta musamman da kwamitin tsaro da kuma Mukaddashin Babban Sufeton 'yan
sanda suka kai wa Shugaban rundunar sojin kasar Laftanar Janar Ibrahim
Attahiru.
Laftanar Janar Ibrahim Attahiru ya bayyana
cewa lallai ya ji dadin wannan ziyara domin ta zo ne a daidai lokacin da yake
da bukata, domin a cewarsa dama akwai bukatar tattaunawa a tsakanin kwamitin da
rundunar sojin kasar da ta 'yan sanda domin samar musu da kayan aiki da kara
musu kwarin gwiwa na aiki wanda hakan zai taimaka musu wajen tunkarar matsalar
tsaron kasarnan.
Wannan
dai ita ce ziyarar mukaddashin Babban Sufeton 'yan sanda Usman Alkali Baba ta
farko tun bayan nadin da aka yi masa, ya ce tabbas hakan zai taimaka a kawo
karshen matsalar 'yan fashin daji da ta sauran muggan ayyuka da ke addabar
kasar.
Mukaddashin Babban Sufeton ya kara
da cewa hadin kai tsakanin bangarorin biyu na da amfani ganin cewa duka al'ummar
kasar sun dogara ne a kansu wajen tabbatar da tsaro.
Yayin
wannan ziyara shugaban kwamitin tsaro na majalisar kasar Sanata Mohammed Ali
Ndume da wasu manyan jami'ai sun tofa nasu albarkacin bakinsu.
No comments