Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa, EFCC na ci gaba da yi wa tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari tambayoyi kan wa...
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa
ta kasa, EFCC na ci gaba da yi wa tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari
tambayoyi kan wasu zarge-zargen cin hanci da rashawa.
An tattaro cewa an rike tsohon
gwamnan a ofishin hukumar na Sakkwato na tsawon awanni takwas har zuwa lokacin
rubuta wannan rahoton a ranar Talata, 20 ga watan Afrilu.
Majiya ta ce an bayar da belin Yari
amma bai iya cika sharuddan belin ba kamar yadda Jaridar Premium Times ta labarto.
Tsohon gwamnan jihar Zamfara,
Abdulaziz Yari, yana hannun hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa
zagon kasa (EFCC).
No comments