Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Jaridar MADOGARA Ta Kaddamar Da Sabon Tambarinta Da Shafin Intanet

Daga Zailani Mustapha A kokarin da Jaridar MADOGARA ke yi wajen bunkasa ayyukanta bisa doron zamani da ka’idar aikin Jarida, jaridar ta sa...

Daga Zailani Mustapha

A kokarin da Jaridar MADOGARA ke yi wajen bunkasa ayyukanta bisa doron zamani da ka’idar aikin Jarida, jaridar ta sauya tambarinta domin ya dace da manufofinta da kudurorinta.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Babban Editan Jaridar, Ammar Muhammad Rajab a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Alhamis din 17 ga watan Agustan 2023.

“mun sauya tambarin ne domin jaridar ta bambanta da sauran shafuka tare da inganta ayyukanmu”, in ji sanarwar.

Sannan har wala yau sanarwar ta ce ta sauya shafin Intanet dinta daga ( www.madogara.com.ng ) zuwa www.jaridarmadogara.com.ng domin gudanar da ayyukan jaridar cikin inganci.

Sanarwar ta kara da cewa; jaridar mallakin kamfanin MASSNOOR MEDIA SERVICES ne. Kuma shafin jaridar na turanci shi ne DAILY STRUGGLE da ake buga a shafin intanet na www.dailystruggle.com.ng wanda ta ce shima a nan gaba za ta zo da sauye-sauye domin bunkasa jaridar. 

No comments