Daga Zainab Rauf, Abuja Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky, ya bayyana alhini da jimami kan mummunar ambaliya da...
Daga Zainab Rauf, Abuja
Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya,
Shaikh Ibraheem Zakzaky, ya bayyana alhini da jimami kan mummunar ambaliya da
ta afkawa garin Mokwa a jihar Neja, wadda ta yi sanadin mutuwar mutane da dama
tare da jikkata wasu da kuma raba da dama da matsugunansu.
Shehin Malamin ya bayyana hakan ne a
cikin wata sanarwar ta’aziyya da ofishinsa ya fitar a ranar Litinin, 2 ga watan
Yunin 2025, inda ya yi addu’o’i ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, tare da
fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata da kuma dawo da kwanciyar
hankali ga duk wadanda lamarin ya shafa.
“sakamakon mummunar ambaliyar ruwa
da ya afku a ƙaramar hukumar Mokwa ta jihar Neja, wanda ya yi sanadiyyar rashin
rayuka, jikkata jama’a tare da hasarar dukiyoyi da dama, Jagora Sheikh Ibraheem
Zakzaky na jajanta ma iyalan dukkan waɗanda wannan ibtila’in ya shafa”, in ji
sanarwar.
“muna addu’ar Allah maɗaukakin Sarki
ya jiƙan waɗanda suka rasu, da samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata; Allah kuma ya
maida sabon arziki ga waɗanda suka yi hasarar dukiya. Allah Ta'ala ya kiyaye
aukuwar irin wannan a nan gaba”, sanarwar ta jaddada.
Shehin Malamin ya kuma yi addu’ar
samun sauki cikin gaggawa ga waɗanda suka jikkata, tare da roƙon Allah Maɗaukaki
ya kare al’umma daga irin wannan masifa a nan gaba.
Ambaliyar wacce ta auku, ta yi
sanadin mummunar barna, tare da jefa al’umma cikin damuwa da tausayawa a fadin
ƙasar, a yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin kai agaji ga waɗanda abin ya shafa.
Sakon ta’aziyyar ya fito ne ta
dandalin ofishin Shehin Malamin @Szakzakyoffice, tare da alamar ƙarfafa zumunci
da tausayi kamar haka: #MokwaFlood, #FreePalestine, #PrayForPalestine, da kuma
#OurMartyrsOurHeroes.
No comments