Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Mun zaɓo ministoci ne bisa cancanta - Tinubu

  Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce ministocin da aka rantsar a yau an zaɓo su ne bisa cancanta domin su taimaka wajen tafiyar da la...

 


Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce ministocin da aka rantsar a yau an zaɓo su ne bisa cancanta domin su taimaka wajen tafiyar da lamurran ƙasar.

Shugaban na Najeriya ya bayyana hakan ne a lokacin da ya yi jawabi bayan rantsar da sabbin ministoci a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

"Ƴan Najeriya na sa ran za ku yi aiki mai inganci kuma za ku sauke nauyin da aka ɗora muku." - In ji Tinubu

Ya ƙara da cewa "Dole ne ku yi aikin da zai sanya ƴan Najeriya su sake amincewa da gwamnati."

Ya bayyana cewa akwai babban nauyi a kan sabbin ministoci ganin irin manyan alƙawurran da gwamnatinsa ta ɗauka.

Shugaban ya kuma buƙaci sabbin ministocin da su yi aiki ba tare da nuna banbanci ba, inda ya ce: ”An ba ku wannan matsayi ne ba domin ɓangaren da kuka fito ku jihonhinku ba, sai dai domin ƙasa baki ɗaya.”

A watan Afrilu ne shugaban na Najeriya ya miƙa wa Majalisar Dattijan ƙasar sunayen mutum 45 domin tantantancewa a matsayin minsitoci.

Bayan haka nan shugaban na Najeriya ya bayyana ma'aikatun da kowane minista zai riƙe gabanin ranar ta yau da ake rantsarwar.

Sai dai ko a ranar Lahadi, shugaban ya fitar da wasu sauye-sauyen da ya yi na ma'aikatu ga wasu sabbin ministocin.

Jerin ministocin Tinubu



Ma’aikatar kuɗi da tattalin arziƙi - Wale Edu

Ma’aikatar sadarwa da ƙirƙire-ƙirƙire da tattalin arziƙin dijital - Bosun Tuani

Ma’aikatar harkokin tattalin arziƙin teku - Bunmi Tunji-Ojo

Ma’aikatar sufuri - Adegboyega Oyetola

Ma’aikatar wutar lantarki - Adebayo Adelabu

Ma’aikatar ma’adanai - Dele Alake

Ma'aikatar shari'a Lateef FagbemiMa’aiktar yada labarai da wayar da kan jama’a – Muhammad Idris

Ministan Ilimi -Yusuf T. Sununu

Karamin ministan gidaje da raya birane -Abdullahi T Gwarzo

Ministan ayyukan gona da samar da abinci -Abubakar Kyari

Ministan Ilimi – Tahir Mamman

Ministan harkokin cikin gida -Sa’idu Alkali

Ministan harkokin waje – Yusuf Tuggar

Ministan lafiya – Farfesa Ali Pate

Ministar al’adu – Barista Hannatu Musawa

Ministan wasanni - John Enoh

Ministan sufurin jirgin sama - Festus Keyamo

Karamar ministar Abuja – Mairiga Mahmud

Ministan Ilimi da fasaha - Uche Nnaji

Ministar harkokin mata – Uju Kennedy

Ministan ayyuka - David Umahi

Ministan ma'aikatar Neja-Delta - Abubakar Momoh

Tinubu ya yi wa ministoci sauyin ma'aikatu

Gabanin rantsar da sabbin ministocin, Shugaba Bola Tinubu ya sanar da sauyin ma'aikatu ga wasu ministocinsa a ranar Lahadi.

Inda aka mayar da Adegboyega Oyetola zuwa ma’aikatar harkokin tattalin arziki mai alaka da teku daga ma’aikatar sufuri.

Shugaban ya mayar da Abubakar Momoh daga ma’aikatar matasa ta tarayya zuwa ma’aikatar raya Neja-Delta.

Sanarwar sauye-sauyen wadda ta fito ta hannun mai taimaka wa shugaban ƙasar kan yaɗa labaru Ajuri Ngelale ta ce yanzu Bunmi Tunji-Ojo ya koma ma’aikatar harkokin cikin gida, Sa’idu Alkali kuma shi ne sabon ministan sufuri.

Bugu da kari, an mayar da Ministocin Ma’aikatar Man Fetur da Gas zuwa Ma’aikatar Albarkatun Man Fetur ta Tarayya inda Sen. Heineken Lokpobiri a yanzu shi ne ƙaramin Ministan man fetur, yayin da kuma Hon. Ekperipe Ekpo shi ne Karamin minista mai kula da ɓangaren 'Gas'.

Hotunan yadda aka rantsar da ministoci








No comments