Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Wike ya yi barazanar rusa gidaje a ranarsa ta farko a ofis

  Sabon ministan babban birnin tarayyar Najeriya - Abuja, Nyesom Wike, ya yi barazanar fara rusa gidajen da aka gina ba bisa ka’ida ba. Wike...

 


Sabon ministan babban birnin tarayyar Najeriya - Abuja, Nyesom Wike, ya yi barazanar fara rusa gidajen da aka gina ba bisa ka’ida ba.

Wike ya bayyana haka ne a jawabinsa na farko bayan rantsar da shi domin soma aiki.

"Idan kun gina gidajenku a wuraren da aka saba ka'ida, sai an rusa su," in ji Wike.

Tsohon gwamnan Ribas din yana cikin ministoci 45 da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da su a fadarsa da ke Abuja.

Wike ya sha alwashin yin tir da tsarin da ke kawo cikas ga taswirar babban birnin tarayyar.

Sabon ministan Abuja ya yi alƙawarin inganta tsaro a babban birnin

Sabon ministan Abuja, Mista Nyesom Wike ya ci alwashin inganta tsaro a babban birnin na Najeriya, jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da shi a kan muƙaminsa.

Tsohon gwamnan na jihar Ribas, ya bayyana takaici kan taɓarɓarewar tsaro a babban birnin, inda ya ce kamata ya yi Abuja ta kasance, birni mafi aminci a Najeriya.

Ya bayyana damuwa kan yadda ake zaman ta-ci-barkatai a sassan birni.

A cewar Wike, wanda ke jawabin kama aiki tare da jami'an ma'aikatar babban birnin, sabon ministan ya ce ba zai lamunci yadda ake kasa kaya a kan titunan Abuja, ba tare da bin tsari ba.

No comments