Sabon ministan babban birnin tarayyar Najeriya - Abuja, Nyesom Wike, ya yi barazanar fara rusa gidajen da aka gina ba bisa ka’ida ba. Wike...
Sabon ministan babban birnin tarayyar Najeriya - Abuja, Nyesom Wike, ya yi barazanar fara rusa gidajen da aka gina ba bisa ka’ida ba.
Wike ya bayyana haka ne a jawabinsa na farko bayan rantsar da shi domin soma aiki.
"Idan kun gina gidajenku a wuraren da aka saba ka'ida, sai an rusa su," in ji Wike.
Tsohon gwamnan Ribas din yana cikin ministoci 45 da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da su a fadarsa da ke Abuja.
Wike ya sha alwashin yin tir da tsarin da ke kawo cikas ga taswirar babban birnin tarayyar.
Sabon ministan Abuja, Mista Nyesom Wike ya ci alwashin inganta tsaro a babban birnin na Najeriya, jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da shi a kan muƙaminsa.
Tsohon gwamnan na jihar Ribas, ya bayyana takaici kan taɓarɓarewar tsaro a babban birnin, inda ya ce kamata ya yi Abuja ta kasance, birni mafi aminci a Najeriya.
Ya bayyana damuwa kan yadda ake zaman ta-ci-barkatai a sassan birni.
A cewar Wike, wanda ke jawabin kama aiki tare da jami'an ma'aikatar babban birnin, sabon ministan ya ce ba zai lamunci yadda ake kasa kaya a kan titunan Abuja, ba tare da bin tsari ba.
No comments