Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Harkar Musulunci Ta Yi Allah-wadai da Kama Shugaban Al’ummar Falasɗinu a Nijeriya, Tana Neman Sakin Sa Nan Take

Daga Zainab Rauf, Abuja Harkar Musulunci a Nijeriya ta yi kakkausar suka da Allah-wadai da kama Ramzy Ibrahim Abusafiah, shugaban al’ummar...


Daga Zainab Rauf, Abuja

Harkar Musulunci a Nijeriya ta yi kakkausar suka da Allah-wadai da kama Ramzy Ibrahim Abusafiah, shugaban al’ummar Falasɗinu da ke Nijeriya, inda ta bukaci a sako shi ba tare da wani sharadi ba, kuma nan take.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Laraba, 27 ga Agusta, wadda Sheikh Sidi Munir Mainasara Sokoto ya sanya wa hannu a madadin jagoran Harkar, Sayyid Ibraheem Zakzaky, ta bayyana wannan kamu a matsayin “abin ƙi, abin Allah-wadai kuma abin da zai iya bata sunan Nijeriya a idon duniya.”

A cewar sanarwar, jami’an tsaron Nijeriya ne suka kama Abusafiah a ranar Juma’a, 22 ga Agusta, 2025. Duk da cewa ba a fitar da wata hujja a hukumance dangane da dalilin kamewar ba, Harkar Musulunci na ganin hakan na da nasaba da wata sabuwar yarjejeniyar tsaro tsakanin Nijeriya da Isra’ila—yarjejeniya da Harkar ta soka ƙwarai.

“Wannan kamu... ta bayyana sabon salo a siyasar diflomasiyyar Nijeriya,” in ji sanarwar. “Wannan saba wa goyon bayan da Nijeriya ke bai wa Falasɗinu ne a tsawon tarihi, kuma haɗari ce babba da ke nuna goyon baya ga wata haramtacciyar ƙasa da ake ƙin amince mata a duniya.”

Harkar Musuluncin ta tunatar da jama’a irin goyon bayan da Nijeriya ta ba Falasɗinu a tarihi, ciki har da amincewar Nijeriya da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cikakken ‘yanci a shekarar 1988, da kuma ƙuri’ar da ta kaɗa a Majalisar Ɗinkin Duniya a 2012 don bai wa Falasɗinu ‘yanci da matsayinta. Haka kuma, ta ambato wata sanarwa daga Ministan Harkokin Waje na Nijeriya, Yusuf Tuggar, a shekarar 2024, inda ya yi Allah-wadai da hare-haren Isra’ila a Gaza yayin wata ziyarar diflomasiyya da ya kai ƙasar Qatar.

Harkar Musulunci ta nuna damuwa kan abin da ta kira “canjin fuska” a harkar diflomasiyyar Nijeriya a ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu, musamman duba da sabuwar alaƙar Nijeriya da abin da Harkar ta nanata da “haramtacciyar ƙasar Isra’ila.”

Sanarwar ta yi nuni da yadda ƙasashen duniya ke ƙara yin Allah-wadai da halayen Isra’ila a Gaza, ciki har da ƙarar kisan kare dangi da Afrika ta Kudu ta shigar da ita gaban Kotun Ƙoli ta Duniya (ICJ), tare da goyon bayan wasu ƙasashe da dama. Haka kuma, ta ambaci takunkumin tattalin arziƙi da ƙasashe kamar Turkiyya da Birtaniya suka ɗora wa Isra’ila a matsayin wata shaida ta yadda ƙasar ke kara fadawa halin kaɗaituwa.

Baya ga bukatar a saki Abusafiah nan take, Harkar Musulunci ta kuma bukaci a gaggauta soke duk wata yarjejeniyar tsaro tsakanin Nijeriya da Isra’ila, tana zargin cewa Isra’ila na amfani da faɗace-faɗacen Afrika domin sayar da makamai da gudanar da leƙen asiri.

“A don haka, muna kiran malamai, marubuta, ‘yan jarida da daukacin ‘yan Nijeriya da su fito fili su nuna rashin amincewa da wannan sauyin fuska a diflomasiyyar Nijeriya,” in ji sanarwar.

Kungiyar ta kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan wata mai albarka na Rabi’ul Awwal—wata da aka saba amfani da shi wajen haɗin kai da tunani—domin nuna adawa da wannan kamu, tare da goyon bayan ƙudurin ‘yancin Falasɗinu. Bikin Mauludi na bana, wanda taken sa shi ne “Haɗa kan Musulmai Wajen Goyon Bayan Falasɗinu”, ana sa ran zai ƙara ƙarfafa wannan kira.

No comments