Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

CAN Ta Dakatar Da Shugabanta Na Gombe Saboda Taya Pantami Murnar Zama 'Farfesa'

  Kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) ta dakatar da shugabanta na jihar Gombe Sunday Congo, saboda wasikar da ya aika wa ministan Sadarwa da ...

 


Kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) ta dakatar da shugabanta na jihar Gombe Sunday Congo, saboda wasikar da ya aika wa ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin zamani, Isa Ali Pantami, inda a ciki yake taya shi murnar zama Farfesa.

A cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan 15 ga Satumba, da Sakataren kungiyar Daramola Bade ya sanya wa hannu, ya sanar da dakatar da Mista Congo saboda zargin wuce gona da iri.

Sanarwar ta ce an fitar da sanarwar ne ba tare da amincewar shugabancinta na kasa ba.

“mun aiko maka wannan wasika don sanar da kai cewa abun da ka yi ya haifar da damuwa a tsakanin 'ya'yan wannan kungiya''.

“Wannan ba dai-dai bane, ka yi ne ba tare da wani izini ba', don haka ana umartarka da ka bar mukaminka nan take', Inji wasikar.


No comments