Dauda Lawal ya zama sabon gwamnan jihar Zamfara bayan ya sha rantsuwar kama aiki a Gusau babban birnin jihar. Ya karbi mulki daga wurin ts...
Dauda Lawal ya zama sabon gwamnan jihar Zamfara bayan ya sha rantsuwar kama aiki a Gusau babban birnin jihar.
Ya karbi mulki daga wurin tsohon gwamnan jihar Bello Mohammed Matawalle.
An yi bikin ne a filin baje koli da ke Gusau, a birnin jihar Zamfara.
Shi ma mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mallam Mani Muni ya sha rantsuwa.
Sabon gwamnan zai soma aiki ne a yayin da jihar ke fama da matsalar tsaro ta 'yan bindiga wadanda ke kashe mutane tare da sace wadansu domin karbar kudin fansha.
No comments