Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Ko Kun San Wane Ne Sabon Sufeto Janar Na 'Yan Sandan Nijeriya?

  Daga Ammar Muhammad Rajab  Shugaban kasa, Bola Tinubu ya kori Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, tare da maye gurbinsa da mata...

 


Daga Ammar Muhammad Rajab 

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya kori Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, tare da maye gurbinsa da mataimakin Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, a matsayin mukaddashinsa.

Shugaban ya kuma amince da murabus din dukkan shugabannin tsaro, masu ba da shawara, Kwanturola-Janar na Kwastam daga aiki tare da kuma maye gurbinsu nan take.

Wadannan wasu muhimman batutuwa ne da ya kamata ku sani game da mukaddashin shugaban 'yan sandan;

An haife shi a ranar 4 ga Satumba, 1964 a Erinja a karamar hukumar Yewa ta Kudu a jihar Ogun.  Egbetokun ya yi karatun digirinsa na farko a fannin lissafi a Jami’ar Legas. Kafin ya shiga aikin ‘yan sandan Nijeriya, ya karantar da ilimin lissafi a Kwalejin Fasaha ta Yaba da ke Legas.

Ya kuma sami digirinsa na biyu a fannin 'Engineering Analysis',  da kuma Babbar Difloma (PGD) a fannin tattalin arzikin man fetur daga Jami’ar Jihar Delta, da kuma MBA a Jami’ar Jihar Legas.

TSOHON JAMI'IN TSARO (CSO) NA TINUBU 

Egbetokun ya soma aikin ‘yan sandan Nijeriya ne a ranar 3 ga Maris, 1990 a matsayin mataimakin Sufeto na ‘yan sanda na Cadet a Course 16. Ya kasance Babban Jami’in Tsaro (CSO) ga Tinubu lokacin da ya zama Gwamnan Jihar Legas a 1999.

SHUGABAN SASHE, JIHA, DA KUMA YANKI

Mukaddashin Sufeto Janar na 'yan sandan ya rike shugabancin sashe da jihohi da dama. Ya kasance Kwamandan Rundunar 'Rapid Response Squad (RRS)' a Legas daga 2005 zuwa 2007, Squadron Kwamanda na 5 PMF a birnin Benin, jami’in yaki da zamba a rundunar a FCT, Kwamandan yankin Oshogbo, Jihar Osun. Kwamandan yankin Gusau na jihar Zamfara, Kwamandan Makarantar horar da ‘yan sanda da ke Ikeja, Legas da mataimakin kwamandan Kwalejin ‘yan sanda da ke Ikeja.

Ya kuma kasance jami'in tuntuba na Kwamishinan 'yan sanda a hedikwatar rundunar da ke Abuja, ya kuma rike Kwamishina mai kula da bangaren abubuwa masu fashewa (EOD), da kuma kwamishinan rundunar ‘yan sandan a jihar Kwara.

Egbetokun ya kuma taba zama mataimakin Sufeto-Janar mai kula da shiyya ta 7 Abuja, mai kula da ‘yan sandan Neja da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Har ya zuwa nadin nan na shi na baya-bayan nan, shi ne mataimakin Sufeto Janar n 'yan sanda (DIG) mai wakiltar shiyyar Kudu maso Yamma a  tawagar gudanar da 'yan sanda.


No comments