Daga Zailani Mustapha Tsohon Kakakin majalisar jihar Kaduna, Honorabul Yusuf Ibrahim Zailani ya yi bayanin yadda suka dakile tsohon gwamna...
Daga Zailani Mustapha
Tsohon Kakakin majalisar jihar Kaduna, Honorabul
Yusuf Ibrahim Zailani ya yi bayanin yadda suka dakile tsohon gwamnan jihar
Kaduna daga rushe kotunan shari’ar Musulunci da kuma kotunan shari’ar gargajiya
a fadin jihar. kamar yadda jaridar MADOGARA ta labarto.
Zailani ya bayyana
hakan ne a jawabin bankwana da ya yi kan kammala wa’adin mulkinsa a matsayin
Kakakin majalisar a ranar Alhamis 8 ga watan Yunin 2023. Inda ya ce ba don
jajircewarsa ba da yanzu tsohon gwamnan ya gadar da fitinar da Allah kadai ya
san inda za ta tsaya.
Zailani ya soma
bayaninsa ne da godiya ga Allah bisa kammala wa’adin mulkinsa a matsayin
Kakakin majalisar lafiya, inda ya ce; “Yau rana ita ce ta karshe a wannan a
majalisa ta Tara. Ya zama dole mugode ma mutanen jihar Kaduna da ‘yan’uwana
‘yan majalisa da suka ba mu dama muka zauna a wannan kujera na tsawon shekaru
uku da ‘yan watanni a matsayina na Kakakin majalisar jihar Kaduna. Ya zama dole
bayan mungode ma ‘yan majalisa, mugode ma ma’aikatan majalisar jihar Kaduna.
Duk nasarar da aka samu wallahi da ba su ba za a samu ba. Da kunci da aka shiga
iri daban-daban amma suka tsaya tsayin daka domin tabbatar da an yi abin da
yakamata”, inji shi.
Ya ci gaba da cewa; “mun
ga abubuwa iri daban-daban mun kuma gode ma Allah, da ya kawo mu irin wannan
rana mai albarka. Sai dai mulki Allah ke da shi, kayanshi ne, ya kan ba wanda
ya so a lokacin da ya so”.
Zailani ya ce ya gamu
da tarnaki iri daban-daban, kuma abubuwa marasa dadi da mai dadi sun faru. “Kuma
ya zama dole ba zan kulle gidan nan ba, sai na yi bayani a kan su. Ina na fito,
ina nake, ina kuma nake fatan mu tafi. Abin da ya fi tayar min da hankali, na
roki duk wanda ya yi min ba daidai ba a jihar Kaduna na sani ko ban sani ba don
Allah ya yafe min. Wanda kuma ya yi min da gangar ko kuma bisa kuskure, wallahi
na yafe mishi”, ya tabbatar.
Sai dai ya ce ko a yau
ya bar majalisar jihar Kaduna to ya gode ma Allah, inda ya yi bayanin dalilan
da yasa ya fada masifu daban-daban a yayin rike da jagoracin Kakakin majalisar
jihar. “Dalili guda daya abin da ya sa na shiga masifu daban-daban; akwai doka
wanda aka so da shi wannan gidan (majalisar), na ci wuya iri daban-daban da ya
ba ni iko na tsaya da goyon bayan ‘yan’uwana ‘yan majalisa dokarnan ba ta
tabbata ba”.
Ya kara da cewa; “Ba
wata doka bane illa doka da aka turo min 30 ga watan Janairu shekara ta 2023
wanda aka turo dokarnan cewa ana son a share kotunan shari’ar Musulunci a jihar
Kaduna, a kori kotunan shari’ar gargajiya a jihar Kaduna wanda bai tabbata ba. Saboda
haka ni ko a nan na tsaya, wallahi tallahi na godema Allah”, ya lurantar.
“duk masifar da na
shiga wannan doka ita ta ja min. Kuma ba ni da na sani ko na minti na daya. Ni
ina da Sarauta na Garkuwar Alkur’ani mai girma a ce na zo na share kotunan
shari’ar Musulunci da kotunan shari’ar gargajiya wanda mutane da yawa sun
hallaka wajen tabbatar da wadannan kotuna guda biyu a ce mu koma Area Court na
da can, wallahi na godema mutanen da suka ba ni dama na zama dan majalisa. Ko
da shi kadai ne aikin da na yi a matsayin dan majalisa” ya ce.
Zailani ya ce tabbas
kudurin wannan doka ma kokarin tada fitina ne a jihar Kaduna; “Domin wannan
abin da ta fita wallahi da fitinar da zai biyo baya a jihar Kaduna Allah kadai
ya sani. Saboda haka wannan doka ina rokon ‘yan’uwana ‘yan majalisa da wani ya
shigar da kuduri na watsi da wannan dokar da aka turo domin ya zama a tarihin
wannan doka an yi watsi da ita”, ya roka.
Bayan wannan rokon da
Zailani ya yi ne, nan take aka yi watsi da dokar, wanda wannan ya zama shi ne
aiki na karshe da Yusuf Ibrahim Zailani ya yi a matsayinsa na Kakakin majalisar
jihar Kaduna.
“wannan doka da tsohon
gwamnan jihar Kaduna ya kawo, an mayar da wannan doka, ba a amince da ita ba.
An yi tir da ita”, ya jaddda.
No comments