Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Kwamitin Tabbatar Da Tsaro A Garin Minna Su Tabbatar Sun Yi Aiki Bisa Tsarin Doka, In ji Kwamishinan Shari'a

Daga Awwal Umar Kontagora An yi kira ga kwamitin tabbatar da tsaro a karamar hukumar Chanchaga da su tabbatar sun gudanar da aikin su bi...



Daga Awwal Umar Kontagora

An yi kira ga kwamitin tabbatar da tsaro a karamar hukumar Chanchaga da su tabbatar sun gudanar da aikin su bisa tsarin doka, duk wanda aka cafke da zargin ta'addanci a tabbatar an dauki cikakken bayaninsa tare da gabatar da shi gaban kuliya cikin awanni arba'in da takwas domin akwai kotunan musamman da gwamnati ta kafa wajen hukunta duk wanda aka kama.

Kwamishinan shari'a kuma Alkalin Alkalai na jihar Neja, Hon. Nasiru Mu'azu ne ya yi kiran kaddamar da kwamitin a fadar Sarkin Minna, Mai Martaba Umar Faruq Bahago a yammacin Talatar nan.

A cewarsa tattara bayanan mai laifi zai bada damar duk wani lokacin da aka samu rahoton ta'addanci za a samu sauke cafke duk wanda ake zargin yana da hannu domin akwai cikakken bayani a kan sa.

Da yake bayani ga manema labarai, shugaban kwamitin, tsohon kaftin din soja, Umar Sanda ya ce kwamitinsa a shirye take ta yi aikin ba sani ba sabo, duk wanda aka cafke shi da laifin ta'addaci wajibi ne ya fuskanci hukunci.

Kaftin Sanda, ya cigaba da cewar a baya ana zargin wasu masu ido da kwalli kan yi amfani da matsayinsu wajen karbo belin masu laifi, a wannan karon ba za mu sanya idanu hakan ya ci gaba da faruwa ba, matakin farko na aikin mu za mu tabbatar mun wayar da kan matasa muhimmancin zaman lafiya, shi yasa a wannan zaman muka gayyaci iyaye da masu ruwa da tsaki dan wayar masu kai kan yin katsalandan a ayyukan mu, duk yaron da aka kama dole ne a hukunta shi, za mu samar da tsare tsaren tsaro ta yadda za mu tabbatar ta'addanci bai samu gindin zama a Minna ba.

Hon. Mohammed Nma Kolo, Jawon Minna, shi ne mai baiwa gwamnan Neja shawara akan harkokin siyasa da tsare tsare, yace yanzu ba lokacin siyasa ba ne, balle wani mai laifi ya labe da sunan siyasa.

Da zaran an gama zabe siyasa ya kare wajibi kowa ya hada kai da gwamnati dan ganin an samu cigaban kasa, ba wani dalilin da zai sa mutum ya dauki mataki yana farautar jama'a, ana zubar da jini tare da kashe rayukan jama'a da yin sace sace.

Duk wanda ya sanya hannu wajen ganin an sake mai laifi wannan tamkar daurewa laifuka gindi ne, dan haka gwamnati ba za ta lamunci duk wani dan siyasa ko wani babban mutum sanya hannu wajen sake mai laifi ba.

Ina kira ga matasa da su sani su ne manyan gobe, ba yadda goben su za ta yi kyau mutum ba su gyara rayuwarsu a yanzu ba.

Kamar yadda aka bayyanawa mai martaba sarkin Minna yanzun akwai aikace aikace da dama da kwamitin za ta gabatar dan samar da zaman lafiya tare da kawo karshen sara suka da kashe jama'a a garin Minna.

Kwamitin dai ya shafi masu rike da Sarautun gargajiya, ‘yan siyasa da jami'an tsaro don ganin an samar da zaman lafiya a Minna.

No comments