Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Auratayya Tsakanin Mabambanta Addini Da Kabila Ne Kawai Zai Dunkule Nijeriya, Inji Lai

  Jaridar MADOGARA   ta labarto cewa; Lai Mohammed, ministan labarai da al’adu na Nijeriya ya bayyana cewa a ranar Alhamis zai gabatar...

 


Jaridar MADOGARA  ta labarto cewa; Lai Mohammed, ministan labarai da al’adu na Nijeriya ya bayyana cewa a ranar Alhamis zai gabatar da shawarwari ga taron da za a yi a Kaduna kan matsalar tsaro ga kuma kwamitin tattalin arziki na kasa, NEC, wanda ya ce daga cikin shawarar da zai bayar shi ne akwai bukatar karfafa alakar auratayya tsakanin kabilu da addinai domin dakushe ballewar Nijeriya.

Lai Mohammed ya ce a karkashin kundin tsarin mulki na Article 15, 3C akwai batun kulla auratayya a tsakanin kabilu da addini ga ‘yan Nijeriya.

“ana bukatar kiristoci su auri musulmi, kabilar Itsekiri ya auri Bahaushe, Bayarrabe ya auri Inyamuri, idan aka samu irin wadannan auratayyan, yana da wuya a iya raba kasarnan”, inji shi.

Lai Mohammed ya bayyana hakan ne a yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai a Hedikwatar Kamfanin dillancin labaran Nijeriya, NAN a shirinsu na NANForum.

 

No comments