Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Majalisar Mashawartan Tinubu Ta Ce A Sayar Da Manyan Kadarorin Gwamnati Domin Biyan Bashin Da Ake Bin Nijeriya

  Shugaba Bola Ahmad Tinubu Daga Ammar Muhammad Rajab Jaridar MADOGARA ta labarto cewa; majalisar ba da shawara kan manufofin Shugaba Bola ...

 

Shugaba Bola Ahmad Tinubu

Daga Ammar Muhammad Rajab

Jaridar MADOGARA ta labarto cewa; majalisar ba da shawara kan manufofin Shugaba Bola Tinubu ta gabatar da shawarar sayar da kadarorin Nijeriya domin daidaita bashin da ake bin gwamnatin tarayya.

Majalisar ba da shawarar, wanda Mista Tinubu ya hada domin tallafa masa wajen samar da ci gaban tattalin arziki mai dorewa, ya kunshi Tokunbo Abiru (a matsayin shugaba), Yemi Cardoso, Sumaila Zubairu da Doris Anite, tare da sanya KPMG a matsayin masu ba da shawara.

Majalisar ta yi kira ga gwamnatin Tinubu da ta kafa wani tsari na cewa duk abin da aka samu daga siyar da kadarorin dole ne a yi amfani da shi wajen daidaita bashin da ake bin gwamnatin tarayya.

Sauran shawarwarin kasafin kudi, a cewar majalisar, sun hada da jera hannun jarin kamfanoni masu dabaru da riba na kamfanin man fetur na kasa wato NNPCL, yin amfani da tsarin ‘blockchain’ domin Æ™irÆ™ira tare da samar da damar yin rajistar filaye na gwamnati da raba yanki da kuma ba da izini daukar nauyin raba wutar lantarki.

Majalisar ta kuma ba da shawarar mayar da hannun jari, rangwame ko sayar da hannun jarin gwamnatin tarayya dake kamfanoni ga abokan hulda da sauran masu zuba jari (watakila tare da zabin saye) domin samar da kudaden shiga cikin kankanin lokaci zuwa matsakaicin lokaci, tare da mai da hankali kan kadarorin da ba su da inganci kamar matatun mai na NNPCL.

Har ila yau, majalisar ta ba da shawarar cewa gwamnati ta koma bangaren bunkasa samar da wutar lantarki mai nagarta wanda zai taimakawa ‘yan kasuwa; tare da kuma gudanar da binciken kwakwaf kan lamuni da ya rage da kuma amfani da kudaden Tarayyar yadda yakamata, misali daidaitawa, asusun haɓɓaka albarkatun Æ™asa, ECA (Asusun danyen man fetur) da dai sauransu.

Bugu da kari, majalisar ta ba da shawarar cewa kamata ya yi gwamnati ta magance satar mai da fasa bututun mai tare da kuma samar da mai da kuma iskar gas sosan gaske.

Majalisar ta kara da cewa dole ne gwamnati ta zurfafa tare da fadada ayyukan kwangilolin tsaro a yankin Neja Delta tare da tura jami’an tsaro na musamman; kara yawan samar da kayayyaki ta hanyar amfani da fasaha domin bin diddigin samar da danyen mai; tare da kaddamar da fasaha domin tabbatar da ingantacciyar hanyar gano danyen man da aka sata a Nijeriya.

Sannan ya ba da shawarar aiwatar da aikin tace gangar mai miliyan biyu a cikin gida a kowacce rana tare da samar da damar bunkasa tattalin arzikin al’ummar da man ke yankinsu.

Ta yi kira ga gwamnati da ta kara kaimi wajen samar da ganga miliyan 4 daga kadarori na ketare da na teku a cikin shekaru hudu tare da bunkasa kudaden shigar danyen mai da kuma tanadin ajiyar danyen mai zuwa asusun ajiyar danyen mai (ECA) da Hukumar kula da zuba jari ta Nijeriya (NSIA).

A cewar majalisar, ya kamata gwamnati ta hanzarta aiwatar da asusun amincewa na al’ummar da man ke yankinsu kamar yadda dokar masana'antar man fetur (PIA), tare da aiwatar da matakan domin ninka yawan iskar Gas (LNG)) daga MTPA miliyan 22 zuwa miliyan 40 na MTPA a cikin shekaru takwas (8).

Majalisar ta kuma ba da shawarar kawar da tallafin man fetur da ake sayarwa ababen hawa.

Domin bayar da damar da ake da ita a fannin ma’adanai, majalisar ta yi kira da a aiwatar da wani tsari na ka'ida da halasta ayyukan hakar ma'adinai da ake yi ba bisa ka'ida tare da kuma bunkasa samar da taswirar masana'antar hakar ma'adinai domin sake fasalin fannin tare da jawo manyan 'yan kasuwa na kasa da kasa.

No comments