Wasu dalibai sun gudanar da zanga-zanga a Gusau babban birnin jihar Zamfara bisa garkuwan da wasu ‘yan bindiga suka yi ma wasu d...
Wasu dalibai sun gudanar da zanga-zanga a Gusau babban birnin jihar Zamfara bisa garkuwan da wasu ‘yan bindiga suka yi ma wasu dalibai guda biyar.
Masu zanga-zangar wadanda mafi yawansu daliban jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau ne, sun rufe kan babban hanyar Zariya zuwa Sokoto domin nuna damuwarsu da halin da suke ciki a yau Asabar.
Wannan lamarin ya janyo matuka motoci da fasinjoji tsayuwar dole domin babu hanyar wucewa
Jihar Zamfara dai na daga cikin jihohin da suka Jima suna fama da matsalar masu garkuwan da mutant domin neman kudin fansa.
No comments