Rahotannin dake shigowa Jaridar MADOGARA na nuni da cewa; shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Shugaban majalisar wakilai Fem...
Rahotannin dake shigowa Jaridar MADOGARA na nuni da cewa; shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Shugaban majalisar wakilai Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma'aikatan fadar Gwamnati.
Tinubu har ya wala yau ya kuma naÉ—a tsohon Gwamnan Benue George Akume kuma tsohon ministan ayyuka na musamman a gwamnatin Buhari a matsayin Sakataren Gwamnatin tarayya.
Sanarwar tabbatar da nadin mukaman na fitowa jim kadan bayan kammala ganawa da gwamnonin APC a fadar gwamnati dake Abuja.
Darakan yada labarai na fadar Gwamnatin, Abiodun Oladunjoye shi ne ya tabbatar da hakan a sanarwar da ya fitar.
Har wala yau Tinubu ya nada Sanata Ibrahim Hassan Hadejia, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa a matsayin mataimakin shugaban ma'aikatan fadar gwamnati.
No comments