Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Gwamna Lawal Ya Karrama Mahajjaciyar Da Ta Tsinci Dala 80,000 A Kasar Saudiyya, Ya Ce Shugaban Kasa Zai Karrama Ta

  Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, a ranar Alhamis, ya karrama mahajacciyar da ta mayar da dala 80,000 da ta tsinta ga mai shi a aikin Ha...

 


Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, a ranar Alhamis, ya karrama mahajacciyar da ta mayar da dala 80,000 da ta tsinta ga mai shi a aikin Hajjin da ya gabata a kasar Saudiyya.

Mahajjaciyar, Hajiya Aishatu 'yan Guru Nahuce daga karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara ta tsinci dala 80,000 kwatankwacin naira miliyan sittin da hudu da dubu dari biyu da arba’in (N64,240,000) sannan ta mika wadannan makudan kudaden ga jami'in hukumar jin dadin alhazai ta Zamfara domin ganin an mayar da kudaden ga mai shi.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya ce gwamnan ya karrama mahajacciyar ne a gaban dukkanin Sarakunan jihar a zauren majalisa da ke gidan gwamnati.

Gwamnan ya kuma bayyana matukar farin cikin gwamnatin jihar bisa gaskiyar da wannan mahajjacciya ta nuna.

“Dukkan al’ummar jihar Zamfara suna alfahari da farin ciki kan abin da Hajiya A’ishatu ta yi a Saudiyya. Ya kara wa daukacin al’ummar Zamfara suna.

“Wannan abin alfahari ne a gare mu ba kawai ga Hajiya A’isha ba, ta rubuta sunanta a cikin litattafan tarihi masu kyau. Irin wannan aiki abin so ne ga duk wani Musulmi mai imani, musamman ma a kasa mai tsarki.

“Mun ga misalin aikin kwarai na gaskiya da ya kamata a yi koyi da shi daga Hajiya A’isha, ki yarda da ni, ba kowa ne zai iya tsintar irin wadannan makudan kudade a wurin da ba kowa, kuma ya mayar da su.

“Gwamnatin jihar Zamfara za ta yi duk abin da yakamata wajen taimakawa iyalan Hajiya Aisha.

“Shugaba Bola Ahmed Tinubu shima zai karrama Hajiya A'isha bisa wannan kyakkyawan aiki na gaskiya.”

Tun da farko, Sarkin Bungudu, Alhaji Hassan Attahiru yayin gabatar da Hajiya A’isha, ya jaddada cewa matakin da ta dauka ya kara mutunta al’ummar Zamfara baki daya.

Hajiya Aisha ita ma ta yi bayanin yadda lamarin ya faru a kasa mai tsarki a Saudiyya.

 

No comments