Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Gwamnan Jihar Zamfara Ya Halarci Taron Majalisar Tattalin Arzikin Ƙasa A Abuja

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal tare da sauran gwamnonin Nijeriya sun halarci taron majalisar tattalin arzikin ƙasa yau, a fa...


Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal tare da sauran gwamnonin Nijeriya sun halarci taron majalisar tattalin arzikin ƙasa yau, a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. 

Hakan na kunshe ne a sanarwar da Sulaiman Bala Idris, Babban Mataimaki na musamman kan harkokin watsa labarai ga Gwamnan jihar Zamfara ya fitar a ranar Alhamis. 

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima ne ya jagoranci zaman, inda aka tattauna muhimman batutuwa na tattalin arziki, musamman hanyoyin samar da sauƙi ga jama'a a wannan halin da ake ciki na hauhawar farashin man fetur. 


No comments