A ranar Alhamis 20 ga watan Yuli, 2023, Shugaban Hukumar Gudanarwa na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN), Far...
A ranar Alhamis 20 ga watan Yuli, 2023, Shugaban Hukumar Gudanarwa na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya (MAAUN), Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, ya jagoranci wasu jami’an gudanarwa na Jami’ar zuwa Katsina domin ziyarar ta’aziyya ga Shugaban Kamfanin Max Air, Alhaji Dahiru Barau Mangal bisa rasuwar matarsa, Hajiya A’isha Mangal.
Hajiya A’isha ta rasu
ne a ranar Asabar, 15 ga Yuli, 2023, a wani asibiti da ke Abuja bayan ta yi fama
da gajeruwar rashin lafiya.
Daga cikin ma’aikatan
gudanarwar da suka raka Farfesa Gwarzo a ziyarar sun hada da Shugaban Jami’ar,
Farfesa (Dr.) Mohammad Israr, mataimakin Shugaba bangaren gudanarwa, Dakta
Habib Awais Abubakar, da mataimakin shugaban jami’ar MAAUN-Maradi, Nijar
bangaren gudanarwa. Dr. Shu’aibu Usman Tanko.
Sauran sun hada da mataimakin
Shugaban Jami’ar Franco-British International University, Kaduna, Farfesa
Abdullahi Muhammad Sabo, Daraktan hadin gwiwa da kulla alaka, Dakta Bala
Muhammad Tukur, sai Dakta Lawal Kankia, Shugaban Tsangayar aikin jarida na jami’ar
MAAUN- Maradi, da Dakta Bala Zango da kuma Shugaban Ofishin huldar kasa da
kasa, Injiniya Bashir Garba, da sauransu.
Yayin da yake jajantawa
hamshakin dan kasuwar na Katsina, Farfesa Gwarzo, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar
jami’o’i masu zaman kansu na Afrika (AAPU), ya bayyana rasuwar Hajiya A’isha a
matsayin babban rashi ba kawai ga danginta kadai ba, har ma da daukacin
al’ummar jihar Katsina.
“Zuciyarmu ta yi nauyi bisa
samun labarin rasuwar masoyiyar matarka Hajiya Aisha ba zato ba tsammani.
“A madadin iyalaina da
kuma Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya da Nijer, muna mika
sakon ta’aziyyarmu zuwa gare ku bisa rasuwarta ba zato ba tsammani.
“Ina son na kuma yi
amfani da wannan damar domin jajanta wa daukacin iyalan marigayiyar bisa wannan
babban rashi da aka yi. Allah madaukakin Sarki ya bai wa daukacin iyali ikon
jure wannan rashin da ba za a iya mayarwa ba,” in ji Farfesa Gwarzo.
Sannan ya roki Allah madaukakin
Sarki da ya gafarta mata kurakuranta, ya shigar da ita a Jannatul Firdausi.
A yayin ziyarar
ta'aziyyar an gudanar da addu'a ta musamman ga mamaciyar inda aka karanta wasu
ayoyin kur'ani mai tsarki.
Marigayi Hajiya A’isha
Mangal ta rasu ta bar mijinta, ‘ya’yanta, da kuma jikoki, kuma tuni aka yi
jana’izarta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a Katsina.
Allah ya jikanta da Rahama,
yasa ta huta, amin.
No comments