Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Fasto Buru Ya Nemi Musulmi Da Kirista Su Rungumi Hadin Kai Da Zaman lafiya

  Daga Ammar Muhammad Rajab Fitaccen Fasto din nan da ke kira ga wanzar da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin addinai, Fasto Yohanna Buru ...

 

Daga Ammar Muhammad Rajab

Fitaccen Fasto din nan da ke kira ga wanzar da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin addinai, Fasto Yohanna Buru ya yi kira ga al’ummar musulmi da kirista a duk inda suke a fadin Nijeriya da su rungumi hadin kai da zaman lafiya a tsakaninsu.

Fasto Yohanna Buru ya bayyana hakan ne a yayin da wakilinmu yake zantawa da shi a Zariya, inda ya jaddada bukatar da yake akwai na wanzar da zaman lafiya a tsakanin musulmi da kirista. Inda ya ce; “ina kira ga al’ummar Nijeriya gaba daya amma ina da magana da musulmi ne da kiristoci sune masu rinjaye a kasarnan. Kuma yawan fitintinu na yawan faruwa a junansu.  Ko rashin yarda ne ko siyasa ne ya shiga ko rashin fahimtar addini ne ko  ba a ilmantu na yadda za a yi zama a kyauta mu’amala da zamantakewa a nuna wa juna kaunar juna, shi ne ya kai ga hakan.

Ya ci gaba da cewa; “ina rokon Allah Ubangiji a cikin hikimarsa da ikonsa ya sa musulmi da kirista su fahimci juna. Domin sune za su zama misali ga sauran masu addinai. Sai kuma a samu mune ba ma zaman lafiya.

“Ya kamata masu littafin Attaura da Zabura ya fito ya nuna misali bisa koyarwar littafi mai tsarki, haka kirista haka musulmi. Duka wadannan ‘ya’yan Annabi Ibrahim ne, kuma masu bin addinin Annabi Ibrahim ne. Ya kamata su zama misali.

A don haka ya yi kira da a zauna lafiya da kowanne mutum; “Idan ma gado ne, to za a raba gado. A bar fada da juna, a gina kasa, a gina juna, a yi taimakekeniya a fahimci juna, a kaunaci juna, a yi gudu tare a tsira tare, shi ne mafita ga addini. Amma ‘yan kananan abubuwan dake raba mu, abubuwan da suka hada mu sun fi yawa. A zauna lafiya ko’ina a Nijeriya”, ya jaddada.

Fasto Yohanna Buru a yayin tattaunawar. 

Sannan ya yi na musamman a Nijeriya ga masu tada kayar baya suna kashe-kashe da garkuwa da jama’a da su ji tsoron Allah su bari a zauna lafiya da juna; “Ina kuma rokon wadanda suke dauke da makamai, don an yi musu rashin adalci, ko ‘yan Boko Haram ne, ko kuwa masu garkuwa da mutane ne, ko kuwa wadanda ake cewa ‘yan fashin daji, muna rokon Allah su tausayawa talakawa, a zauna lafiya.

“Kuma a yi adalci a kowanne mataki. Idan Musulmi ne ka yi masa adalci. Idan kirista ne ka yi masa adalci, ita ce mafita ita ce zaman lafiya. Kuma mu koma ga Allah mu yi tuban gaskiya. Don mun riga mun saba ma Allah. 

No comments