Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Yadda 'Yan Bindiga Suka Sake Kashe Mutum Biyu A Kaduna

  Daga Muhammad Farouk  Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe mutum biyu tare da raunata wasu maza shida...

 


Daga Muhammad Farouk 

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe mutum biyu tare da raunata wasu maza shida a wasu hare-hare daban-daban da suka kai kananan hukumomin Chikun da Kajuru ta jihar.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Samuel Aruwan ne ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Talata a Kaduna.

Mista Aruwan ya ce jami'an tsaro sun ba da rahoton cewa 'yan bindiga sun mamaye Mazari, wani gari kusa da Buruku a karamar hukumar Chikun, mutum daya ya mutu a harin, sannan wasu uku sun jikkata.

Ya bayyana cewa a wani lamarin, yan fashin sun kai hari a kauyen Doka, karamar hukumar Kajuru, sun kashe mutum daya tare da raunata wasu uku.

Jihar Kaduna dai na daya daga cikin jihohin da ke fama da matsalar 'yan bindiga a jihohin kasarnan. Kuma daruruwan mutane ne 'yan bindigar suka kashe ko suka yi garkuwa da su a cikin' ‘yan shekarun nan.

Sauran jihohin da irin wannan ta'addancin ya shafa sun hada da Neja, Zamfara da Katsina da Sakkwato.


No comments