Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Amnesty International Ta Caccaki Tinubu Kan Rashin Tsaro

Ƙungiyar Amnesty International ta ce sace fiye da ƴan gudun hijira a jihar Borno da ɗalibai ɗari biyu da tamanin da bakwai da ma...

Ƙungiyar Amnesty International ta ce sace fiye da ƴan gudun hijira a jihar Borno da ɗalibai ɗari biyu da tamanin da bakwai da malamai a yankin Kuriga a jihar Kaduna na nuna gazawar hukumomin Najeriya na kare al'umma daga hare-haren ƴan bindiga da suka kashe dubban ƴan ƙasar cikin shekara biyar da ta gabata.


Ƙungiyar, cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma'a ta hannun shugabanta a Najeriya, Isa Sanusi, ta buƙaci gwamnatin Najeriya ta yi duk mai yiwuwa domin kuɓutar da mutanen da aka sace domin haɗa su da iyalansu.


A cewar ƙungiyar, dole ne hukumomi su gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa kan yawaitar sace-sacen da ake yi a sassa da dama na Najeriya tare da gabatar da sakamakon binciken ga al'umma sannan su tabbatar an hukunta waɗanda aka samu da hannu a garkuwa da mutane.


Amnesty ta ce, "sace-sacen mutane da dama a baya-bayan nan ƙarara sun nuna cewa shugaba Bola Tinubu da gwamnatinsa ba su da tsayayyen tsari na kawo ƙarshen miyagun laifukan ƴan bindiga da ke cin karensu babu babbaka a sassan jihohin Najeriya. Duk matakan tsaron da shugaba Tinubu da gwamnatinsa ke aiwatarwa ba sa tasiri," in ji Isa Sanusi.


"Ganin yadda matsalar tsaro ke ƙaruwa a Najeriya a yanzu, a bayyane take cewa batun kare rayuwa da dukiyoyin al'umma ya na ƙasa cikin jerin abubuwan da gwamnati ta sa a gaba. Bai kamata a ƙyale mutane su zauna cikin fargaba da tsoron hari da garkuwa ba.


Yawan gazawar hukumomin Najeriya wajen kare mutane abu ne da ba za a taɓa amincewa da shi ba kuma dole ne a kawo ƙarshen sa," kamar yadda sanarwar ta bayyana.


Amnesty ta kuma yi kira da a tabbatar da waÉ—anda ke da nauyin samar da tsaro a yankunan da aka yi sace-sacen jama'a su yi bayani kan gazawar da ta jefa rayuwar É—aruruwan mutane cikin haÉ—ari.


A ranar Alhamis ne wasu ƴan bindiga suka kai hari kan wata makarantar Firamare a Kuriga da ke jihar Kaduna inda suka sace ɗalibai kimanin 287 da malaminsu guda ɗaya, sai dai malamin ya samu kuɓuta sai kuma ɗalibi guda da ya mutu.

No comments